Yahaya Bello
Jigon PDP a Najeriya, Segun Showunmi ya koka kan yadda Shugaba Bola Tinubu ya ci amanar Nasir El-Rufai da Yahaya Bello kan halin da suke ciki a yanzu.
An samu aukuwar wani mummunan hatsarin mota a kan hanyar Okene-Lokoja da ke jihar Kogi. Hatsarin motan ya yi sanadiyyar salwantar da rayukan mutum 19.
Tsohon gwamnan jihar Benuwai, Samuel Ortom, ya shawarci Alhaji Yahaya Bello da ya daina wasan buyan da yake yi, ya fito ya kai kansa ga hukumar EFCC.
Lauya kuma dan gwagwarmaya, Deji Adeyanju, ya yi gargadin cewa idan hukumar EFCC ba ta yi taka tsan-tsan ba, za ta iya rusa shari'ar Yahaya Bello.
Tsohon shugaban jam'iyyar APC, Sanata Adams Oshiomole ya caccaki tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello da yaronsa, Gwamna Usman Ododo kan saɓa dokar ƙasa.
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, ta caccaki tsohon gwamnan jihar Kogi kan kin mika kansa ga hukumar EFCC domin a bincike shi.
Babbar kotun jihar Kogi ta umarci shugaban hukumar EFCC, Ola Olukoyede ya hallara a gabanta kan saɓa doka da ya yi kan binciken tsohon gwamnan jihar, Yahaya Bello.
Tsohon gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, ya musanta zargin da hukumar EFCC ta yi na ya biya wa 'ya'yansa kudin makaranta daga asusun jihar Kogi.
Makarantar kasa-da-kasa ta Amurka da ke Abuja (AISA) ta aika wasika ga hukumar EFCC inda ta nemi mayar da $760,000 na kudin makarantar ƴaƴan Yahaya Bello.
Yahaya Bello
Samu kari