Yan bindiga
Gwamnatin jihar Kebbi ta musanta batun cewa 'yan bindiga sun kai kazamin hari a jihar. Ta bayyana cewa babu kamshin gaskiya a cikin rahotannin kai harin.
Malumfashi, Funtua da Bakori sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindiga domin kawo ƙarshen hare-hare da sace-sace a Katsina.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a jihar Nasarawa. 'Yan bindigan sun hallaka mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba.
Rahotanni sun tabbatar da cewa yan bindiga sun kai mummunan hari a garin Makuku, karamar hukumar Sakaba, Jihar Kebbi, inda suka kashe mutane da dama.
'Yan bindiga dauke da makamai sun yi wa jami'an 'yan sa-kai na CJTF kwanton bauna a jihar Zamfara. Miyagun sun hallaka jami'an tsaron a artabun da aka yi.
’Yan sandan Kano sun ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kano da Kaduna, yayin da CP Bakori ya jaddada cewa ba za a bari masu laifi su samu mafaka ba.
Wasu yan bindiga sun kai hari a wani masallaci da ke Gidan Lado a karamar hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina inda suka hallaka mutane biyu yayin harin.
Dakarun sojojin Najeriya masu aikin samar da tsaro sun samu nasara kan 'yan bindiga a jihar Sokoto. Sojojin sun kashe tsageru masu yawa yayin artabun da aka yi.
Jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya sun samu nasarar cafke wasu mutane da ake zargin akwai hannunsu kan kisan da aka yi wata 'yar jarida a birnin tarayya Abuja.
Yan bindiga
Samu kari