Jihar Borno
Babban daraktan hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Borno, Barkindo Mohammed ya ce shi da jami'ansa sun maƙale a wani da wuri da suka je bada agaji.
A safiyar Talata ne jama'ar Maiduguri a jihar Borno su ka wayi gari da ambaliya mafi muni a shekaru 30, inda ta lalata muhimman wurare, har da makabartu.
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bada tabbacin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta magance kalubalen ambaliyar ruwa a Najeriya.
Sanata Ali Ndume ya nuna alhininsa kan ambaliyar ruwan da ta auku a birnin Maiduguri na jihar Borno. Sanatan ya bukaci gwamnatin tarayya ta kai dauki a jihar.
Mahukuntan jami'ar Borno (UNIMAID) sun dauki matakin rufe jami'ar har sai abin da hali ya yi sakamakon ambaliyar ruwan da aka yi a birnin Maidiguri na jihar.
A wannan labarin, daurarrun da ba a kai ga sanin adadinsu ba sun samu damar tserewa daga kurkukun da aka ajiye su bisa laifuffuka daban-daban a Borno.
Shugaba Bola Tinubu ya umarci hukumar NEMA ta gaggauta kai dauki ga wadanda ambaliyar ruwa ta rutsa da su a Maiduduri, yana mai jajantawa gwamnatin Borno.
Ambaliyar ruwa ta rusa gidan dabbobi da ke Maiduguri a jihar Borno. Dabbobi kamar kada da macizai sun shiga gari ta cikin ruwa. Kashi 80 na dabbobi sun mutu.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce shugaban kasa Bola Tinubu ya umarce shi da ya bar Abuja zuwa birnin Maiduguri domin duba ambaliyar da ta faru.
Jihar Borno
Samu kari