An Gano Jam’iyyu 2 da Atiku, Kwankwaso Za Su Iya Komawa saboda Tsaro Kafin 2027
- Wasu rahotanni sun nuna cewa Atiku Abubakar, Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso na shirin barin ADC gabanin zaben 2027
- Rikicin shugabanci da matakin INEC ya jefa ADC cikin rudani mai tsanani wanda ake fargabar zai iya jawo mata asara a zaben
- Majiyoyi sun ce yan siyasar na duba yiwuwar komawa jam’iyyu 2 a matsayin mafita domin gudun ka da lokaci ya kure masu
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Rahotanni sun nuna cewa manyan ‘yan adawa a Najeriya na duba yiwuwar barin jam’iyyar ADC gabanin babban zaben 2027.
Cikin manyan jagororin da ke tattaunawa akwai Atiku Abubakar, Peter Obi da kuma Rabiu Musa Kwankwaso.

Source: Twitter
Musabbabin neman mafita ga Atiku, Kwankwaso daga ADC
An ce wannan mataki na da nasaba da rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar ADC, wanda ya janyo rikice-rikicen cikin gida, cewar rahoton The Guardian.
Hakan ya kara tsananta ne bayan da INEC ta dakatar da amincewa da dukkan bangarorin shugabancin jam’iyyar.
Matakin ya biyo bayan hukuncin kotun daukaka kara da kuma karar da ake yi kan tsarin shugabancin jam’iyyar.
Masana harkokin siyasa sun yi gargadin cewa wannan rikici na iya hana ADC damar tsayar da ‘yan takara a zaben 2027.
Sun ce idan aka ci gaba da wannan hali, jam’iyyar na iya fuskantar matsaloli wajen shiga zaben shugaban kasa, gwamnoni da ‘yan majalisa.
Majiyoyi sun bayyana cewa shari’o’in da ke gudana na iya shafar duk wani dan takara da zai tsaya karkashin jam’iyyar ADC.
Majiyar ta ce:
“Idan wannan rikici ya ci gaba, kuma mambobi suka tsaya takara karkashin ADC, sannan daga baya aka soke amincewa da jam’iyyar, ba za su iya kawai sauya sheka zuwa wata jam’iyya ba.”

Source: Facebook
Jam'iyyun da ake sa ran za su koma
Hakan ya sa shugabannin ‘yan adawa suka fara tattaunawa a boye domin nemo mafita kafin lokaci ya kure musu.
Ana sa ran za su gudanar da wasu muhimman tarurruka a Abuja bayan hutun 'Easter' domin yanke hukunci kan makomar siyasa.
Rahotanni sun ce suna duba yiwuwar amfani da jam’iyyun APP da kuma NDC a matsayin mafita.
Masana sun ce matakin da za su dauka na iya sauya yanayin siyasar Najeriya gabanin zaben 2027 wanda ake ganin zai yi matukar zafi sosai.
Sanata Rabiu Kwankwaso shi ne na karshe da ya dawo ADC a cikin jiga-jigan siyasar Najeriya bayan murabus daga jam'iyyar NNPP da ya yi takara a zaben 2023.
Jam'iyyar adawa na zawarcin Atiku, Kwankwaso
A baya, an ji cewa wata jam’iyyar adawa a Najeriya ta bukaci manyan ‘yan adawa kamar Atiku Abubakar, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso su dawo cikinta.
Jam'iyyar ta bayyana haka ne domin ceto dimokuradiyya a Najeriya wanda ake zargin ana neman rikita jam'iyyun hamayya.
Hakan na zuwa ne yayin da jam'iyyar ADC ta sake burmawa cikin matsala wanda ake zargin gwamnatin APC da hannu a cikin rikicin da take fama da shi.
Asali: Legit.ng

