Aikin Gama Ya Gama, Gwamna Abba Ya Sanar da Jam'iyyar da Zai Koma bayan Barin NNPP

Aikin Gama Ya Gama, Gwamna Abba Ya Sanar da Jam'iyyar da Zai Koma bayan Barin NNPP

Kano, Nigeria - Bayan tsawon lokaci ana rade-radi, gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yuauf ya kammala duk wasu shirye-shirye kuma ya tabbatar da zai koma jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba ya fice daga jam'iyyar NNPP a ranar Juma'a da ta gabata, 23 ga watan Janairu, 2026, lamarin da ya kara zafafa dambarwar siyasar Kano.

Gwamna Abba.
Gwamna Abba Kabir Yusuf yana dagawa masoya hannu a taron raba babura a gidan gwamnatin Kano Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Mai magana da yawun gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanar a shafinsa na Facebook cewa Gwamna Abba Kabir zai koma jam'iyyar APC ranar Litinin mai zuwa.

Sanusi Bature ya ce Gwamna Abba ya shirya tsaf domin komawa jam’iyyar APC) a ranar Litinin, 26 ga Janairu, 2026, biyo bayan murabus din da ya yi daga NNPP) a ranar Juma’ar da ta gabata.

Sanarwar ta tunatar da jama'a cewa Abba ya fara shiga jam’iyyar APC ne a shekarar 2014, inda ya lashe zaben fidda gwani na takarar sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya, matsayin da daga baya ya janye wa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Kara karanta wannan

Zance ya kare: 'Yan Majalisar Kano 22 sun bayyana matsayarsu kan tafiyar Gwamna Abba

An bayyana cewa bayan shekaru na gwagwarmayar siyasa a fage daban-daban, ciki har da zamansa na baya-bayan nan a NNPP, a yanzu Gwamna Abba zai sake komawa APC.

Kalakin gwmanan ya ce yanayin tafiyar da mulki na yanzu, bukatar hadin kan kasa, da ci gaba sun sanya ya zama dole Abba Gida-Gida ya koma APC, wadda ya bayyana a matsayin gida kuma dandali mai nagarta.

Gwamna Abba ya bayyana cewa komawa APC za ta kara karfafa hadin gwiwa tsakanin Kano da Gwamnatin Tarayya, sannan ta hanzarta ci gaban ayyukan ababen more rayuwa, inganta tsaro, da kyautata rayuwar al’umma a fadin jihar Kano.

Ya kara da cewa wannan shawara za ta karfafa kwanciyar hankali ta siyasa da kuma hadin kai a jihar Kano.

A ranar Litinin, 26 ga Janairu, 2026, gwamnan zai yi rajista a hukumance a matsayin dan jam’iyyar APC a Kano, tare da mambobin majalisar dokokin jihar 22, da yan majalisar wakilai ta tarayya guda takwas.

Haka zalika, ana sa ran shugabannin kananan hukumomi guda 44 za su marawa gwamnan baya zuwa APC.

Haka kuma ana sa ran zai kaddamar da shirin rajistar mambobin jam’iyyar APC ta yanar gizo a hukumance.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262