Hukumar BOSIEC Ta Sanar da Sakamakon Zaben Kananan Hukumomin Jihar Borno

Hukumar BOSIEC Ta Sanar da Sakamakon Zaben Kananan Hukumomin Jihar Borno

  • Hukumar zabe ta jihar Borno ta sanar da sakamakon zaben kananan hukumomin da aka gudanar ranar Asabar, 13 ga watan Disamba, 2025
  • Jam'iyyar APC ta samu nasarar lashe dukkan kujerun ciyamomi da kansilolin a fadin kananan hukumomi 27 na jihar Borno
  • Tun a ranar Asabar, Gwamna Babagana Umaru Zulum ya bayyana cewa yana da kwarin gwiwar APC za ta samu nasara a zaben

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Borno, Nigeria - A karshen makon da ya gabata ne hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Borno ta gudanar da zaben kananan hukumomi a fadin jihar da ke Arewa maso Gabas.

Zaben dai ya gudana a fadin kananan hukumomi 27 da ke jihar Borno a ranar Asabar, 13 ga watan Disamba, 2025.

Gwamna Zulum.
Gwamna Babagana Umaru Zulum lokacin da ya kada kuri'a a zaben kananan hukumomin Borno da tambarin APC Hoto: Babagana Umaru Zulum
Source: Facebook

An sanar da sakamakon zaben Borno

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa jam’iyyar APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi da na kansiloli a kananan hukumomi 27 na Jihar Borno.

Kara karanta wannan

Kefas: Gwamnan da fice daga PDP kwanan nan ya yanki katin zama ɗan jam'iyyar APC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Borno (BOSIEC), Dr. Tahir Shettima, shi ne ya sanar da sakamakon zaben a yammacin yau Litinin a Maiduguri.

Dr. Tahir ya jero sakamakon zaben ne yayin da yake yi wa manema labarai jawabi a hedikwatar hukumar BOSIEC da ke Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

BOSIEC ta ce an yi zabe cikin lumana

Ya kuma tabbatar da cewa jama'a sun ba da hadin kai, an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana a fadin mazabun jihar.

A cewarsa, hukumar BOSIEC da yake jagoranta, ta gudanar da zaben ne bisa tanade-tanaden da suka dace na Dokar Zabe ta 2022.

Ya yaba wa jam’iyyun siyasa da suka fafata zaben, tare da sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da jami’an tsaro, kungiyoyin farar hula, ‘yan jarida da kuma kungiyar hadakar jam'iyyu (IPAC) na Jihar Borno.

A cewarsa, zaben ya gudana cikin lumana tare da kammala shi cikin nasara sakamakon bisa jajircewar da masu da tsaki suka yi.

Kara karanta wannan

Matawalle: Kungiya ta ba Tinubu shawarar abin da ya dace da karamin Ministan tsaro

Hukumar BOSIEC ta yabawa Gwamna Zulum

Dr. Tahir ya kuma jinjinawa Gwamna Babagana Umara Zulum, bisa jajircewarsa wajen karfafa dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi ta hanyar samar da kudaden da aka yi amfani da su wajen gudanar da zabukan.

Ya bukaci zababbun shugabannin kananan hukumomin da kansiloli da su tabbatar da kafa nagartaccen wakilci ta hanyar kawo alfanun dimokuradiyya ga al’umma a matakin tushe.

Gwamna Zulum.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum Hoto: @ProfZulum
Source: Facebook

Tun farko, Zulum, ya bayyana a ranar Asabar, yayin da yake kada kuri’arsa a Mafa, garinsu na haihuwa, cewa jam’iyyarsa APC za ta yi nasara a zaben, cewar rahoton The Cable.

PDP ta tsame kanta daga zaben Borno

A baya, kun ji cewa jam'iyyar PDP ta ce ba za ta shiga zaben kananan hukumomi da hukumar zabe ta BOSIEC za ta gudanar a jihar Borno a ranar Asabar ba.

Jam'yyar PDP ta dauki wannan mataki ne bayan da ta yi zargin cewa hukumar zaɓen jihar ba za ta yi adalci ba, kuma an tsuga kudi a takardun neman takara.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar APC ta cimma matsaya, ta tsaida 'dan takarar gwamnan Osun a zaben 2026

PDP ta ce BOSIEC ta gaza ba jam'iyyun adawa tabbacin cewa za ta gudanar da sahihin zabe, don haka tana zargin ba za ta yi adalci ba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262