Taron Siyasa: Ƴan Takarar Gwamna, Ƴan Majalisun Tarayya Sun Sauya Sheka zuwa APC

Taron Siyasa: Ƴan Takarar Gwamna, Ƴan Majalisun Tarayya Sun Sauya Sheka zuwa APC

  • Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, shugaban APC na kasa, sun karɓi kusoshin 'yan siyasa da suka shiga APC
  • Wadanda suka sauya shekar sun hada da Sanata Istifanus Gyang, kusoshin PDP, NNPP, LP, da 'yan takarar gwamna
  • Akpabio ya ce zuwan Prof. Nentawe a matsayin Shugaban APC na kasa zai baiwa jam'iyyar nasara a babban zaben 2027

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Filato - Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, tare da shugaban APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, sun karɓi sababbin ’yan jam’iyya daga jam’iyyu daban-daban a Plateau.

Lamarin ya faru ne a babban dandalin taro na Jos Polo Field, inda dubban magoya baya suka hallara domin tarbar mutanen da suka sauya sheƙa daga PDP, LP, PRP, ADC da NNPP.

Daruruwan magoya bayan jam'iyyun siyasa 5 sun sauya sheka zuwa APC a Filato
Shugaban APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda a taron karbar 'yan adawa zuwa APC a Filato. Hoto: @OfficialAPCNg
Source: Twitter

Fitattun ’yan siyasa sun sauya sheƙa

Kara karanta wannan

Nentawe: Shugaban APC ya fadi jihar da jam'iyyar za ta kwace a zaben 2207

Wannan bayani ya fito ne daga wata sanarwa da mai magana da yawun Akpabio, Anietie Ekong, ya fitar a ranar Lahadi, in ji rahoton Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta bayyana cewa daga cikin wadanda suka sauya sheƙar akwai Sanata Istifanus Gyang, wanda ya wakilci Plateau ta Arewa a Majalisar Dattawa.

Sauran sun hada da tsohon Darakta-Janar na yakin neman zaben PDP a 2023, Latep Dabang; dan takarar gwamna na Lp a 2023, Dr. Patrick Dakum; da tsohon dan takarar NNPP, Alfred Dabwam.

Sauran sun hada da Hon. Fom Dalyop, dan majalisa mai wakiltar Riyom/Barkin Ladi; Hon. Ajang Alfred Ilya, na Jos ta Kudu/Jos ta Gabas; da Hon. Daniel Asama Ago, na Bassa/Jos ta Arewa, tare da sauran masu sauya sheƙa da dama.

Akpabio: “Plateau gaba ɗaya APC ce daga yau”

Akpabio, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a wajen taron, ya ce fitowar Prof. Nentawe a matsayin Shugaban APC ta kasa ya kawo sabuwar nasara ga jam’iyyar a Plateau.

Ya ce:

“Tunanina da idona sun tabbatar min cewa daga yau Plateau ta koma ta APC gaba ɗaya. Zuwa 2027, Plateau za ta ba APC nasara.”

Kara karanta wannan

Turaki: PDP ta zabi sabon shugaban jam'iyyar, ya fadi yadda zai kawo sauyi

Ya kara da cewa jam’iyyar ta samu manyan “kusoshi na siyasa,” ciki har da ’yan takarar gwamna da dama, ’yan majalisar tarayya na baya da na yanzu, da kuma jagororin PDP da LP da suka sauya sheƙa.

Sanata Godswill Akpabio ya ce APC za ta samu nasara a Filato a zaben 2027
Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio. Hoto: @nigeriasenate
Source: Twitter

“Tinubu ya zabi jarumi mai gaskiya” — Akpabio

Akpabio ya yaba wa Shugaba Tinubu saboda nada Farfesa Nentawe, yana mai cewa shugabancin Nentawe ya fara nuna tasiri kafin ma a shiga babban zabe.

Ya ce:

“Shugaban kasa ya samo mutum mai jarumta da nagarta. Nentawe ya jawo nasarar APC a Plateau kafin ma a kai ga zabe."

Ya kuma kara da cewa gwamnatin Tinubu ta dauki dukkan matakai na ganin an magance matsalolin tsaro a garuruwan jihar Plateau.

Gwamnan Filato zai koma APC?

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Jagororin APC a Filato sun ce ba za su amince da duk wani yunkuri daga Gwamna Caleb Mutfwang na PDP a kan sauya sheka ba.

Wannan matsaya na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da rade-radin sauya shekar wasu gwamnoni daga PDP zuwa APC.

A wani taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da aka gudanar a Crest Hotel, Jos, shugabannin jam’iyyar karkashin sun ce gwamnan bai da gurbi a cikinsu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com