Malami Ya Debo Ruwan Dafa Kansa, 'Yan Majalisa Sun Nemi Jami'an Tsaro su Kama Shi
- Rikicin siyasar jihar Kebbi ya kara kamari tun bayan farmakin da ake zargin an kai wa tsohon Antoni Janar, Abubakar Malami
- Tawagar yan Majalisar Tarayya daga Kebbi sun yi watsi da zarge-zargen da Malami SAN ya yi wa Gwamna Nasir Idris
- Sun bukaci hukumomin tsaro su kama tsohon babban lauyan na gwamnati domin ya yi bayani kan abubuwan da ya fada a korafinsa
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kebbi - Sanatoci da yan Majalisar Wakilai daga jihar Kebbi sun bukaci hukumomin tsaro su cafke tsohon Ministan Sharia kuma Antoni Janar, Abubakar Malami.
Tawagar yan Majalisar Tarayya da suka fito da Kebbi sun bukaci a gurfanar da Malami a gaban kotun kan zarge-zargen da ake masa na tayar da zaune tsaye a makon jiya.

Source: Twitter
'Yan Majalisar Tarayya na tare da Kauran Gwandu
Sanata Mai Wakiltar Kebbi ta Tsakiya, Adamu Alieru ne ya bayyana haka da yake zantawa da manema labarai a Abuja, kamar yadda Vanguard ta rauwaito.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A madadin duka yan Majalisar Tarayya na Kebbi, Sanata Adamu Aliero, ya yi watsi korafin da Malami ya shigar a ranar 10 ga Satumba, 2025.
Ya kuma jaddada goyon bayansu ga Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi a ƙoƙarinsa na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar.
'Yan Majalisa sun yi fatali da korafin Abubakar Malami
Sanata Aliero, wanda sauran Sanatoci biyu da ‘yan majalisar wakilai na Kebbi suka raka shi, ya ce:
“Abubakar Malami (SAN) ya zargi Gwamna Nasir Idris (Kauran Gwandu) da wasu ‘yan siyasa da shigo da ‘yan daba, mayakan haya daga ƙasashen waje da kuma safarar makamai a asirce cikin jihar Kebbi.
"Muna son fayyace cewa waɗannan zarge-zargen ba gaskiya ba ne, ba su da tushe, kuma an yi su ne saboda siyasa.
Wani yunƙuri ne na Malami, wanda yanzu ya zama jagoran jam’iyyar adawa ta bogi a Kebbi, domin ruguza zaman lafiya da ci gaban da jama’armu ke morewa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Nasir Idris.”

Kara karanta wannan
Ganduje ya kafa kwamiti, zai binciki gwamnatin Kano kan korar kwamandojin Hisbah 44
- Innji Adamu Aliero.
An zargi Abubukar Malami da tada hankula
Sanata Aliero ya kara da cewa suna da shaida cewa a lokacin da Malami zai je ta’aziyya a Birnin Kebbi, ya ɗauko ‘yan daba daga Sokoto, Koko da Rara don su raka shi.
Ya ce a hanya suka kai hari a ofishin jam’iyyar APC na jihar da duwatsu tare da rera kalamai marasa dadi kan mai girma gwamna, in ji rahoton Daily Post.

Source: Facebook
"Wannan ya haifar da tashin hankali tsakaninsu da magoya bayan APC, abin da bai taɓa faruwa ba a tarihin siyasar Kebbi da aka fi sani da zaman lafiya," in ji Aliero.
Bisa haka ne, Sanata Aliero ya bukaci hukumomin tsaro su gayyaci Malami domin ya yi bayani kan zarge-zargen da ya yi, sannan su gurfanar da shi a kotu.
Zargin da Malami ya yiwa gwamnan Kebbi
A baya, kun ji cewa tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami ya shigar da korafi gaban mai ba shugaban kasa shawara kan tsaro da shugabannin hukumomin tsaron cikin gida.

Kara karanta wannan
Babbar magana: Malami ya zargi gwamna da wasu yan siyasa da alaka da 'yan Ta'adda
Malami, wanda shi ne jagoran jam’iyyar ADC a jihar Kebbi, ya shigar da korafi kan abin da ya bayyana a matsayin shirin da ake yi na tayar da hankali jama'a.
Malami ya kuma zargi Gwamna Nasir Idris da mukarrabansa da da hannu wajen kai masa hari, tare da yin zargin cewa suna da alaƙa da ƙungiyar ta’addanci ta Lakurawa.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng
