Rigima Ta Kunno Kai a ADC, an Dakatar Shugaban Jam'iyya da wasu Manyan Jagorori 2

Rigima Ta Kunno Kai a ADC, an Dakatar Shugaban Jam'iyya da wasu Manyan Jagorori 2

  • Jam'iyyar hadaka ta ADC ta samu kanta a rikicin siyasa tsakanin tsofaffin 'ya'yanta da sababbin da suka shigo
  • Sakataren yada labarai na ADC a Kebbi, ya sanar da dakatar da shugaba, mataimaki da sakatariyar jam'iyyar
  • Ya zarge su da yin abubuwa ba tare da shawara ba tare da jawo 'yan siyasar Abuja wadanda ke son mamaye jam'iyyar

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kebbi - Rikicin siyasa ya kunno kai a jam’iyyar ADC ta jihar Kebbi tun bayan shigowar sababbin ’yan jam’iyya.

Tsofaffin jagororin jam’iyyar ADC a jihar sun dakatar da shugaban jam’iyyar, Injiniya Sufiyanu Bala, mataimakinsa Junaidu Muhammed Mudi, da kuma sakatariyar jam’iyyar, Hauwa Muhammed.

Rikici ya balle a jam'iyyar ADC ta jihar Kebbi
An dakatar da shugaban ADC a jihar Kebbi Hoto: @atiku
Asali: Facebook

Sakataren yada labarai na jam’iyyar, Jamilu Muhammed, ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a birnin Kebbi, cewar rahoton jaridar Vanguard.

Kara karanta wannan

Rikicin cikin gida: PDP ta amince da bukatun Wike, an gano dalili

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An dakatar da shugaban ADC a Kogi

Jamilu Muhammad ya zargi kwamitin gudanarwa da Sufiyanu ke jagoranta da yanke shawara ba tare da tuntubar shugabannin jam’iyyar ba, tare da gudanar da ayyukan hukuma ba tare da samun amincewar kwamitin koli na jam’iyyar ba.

Ya ce an kira taron ne domin sanar da dakatar da Sufiyanu Bala, mataimakinsa, da sakatariyar jam’iyya, Hauwa Muhammed daga jam’iyyar nan take.

Ya kuma yi zargin cewa shugabancin nasu ne ya bai wa ’yan siyasar Abuja masu yawo damar mamaye jam’iyyar, lamarin da wadanda suka assasa jam’iyyar ke adawa da shi sosai.

"Ba za mu bari bayan gina jam’iyyar zuwa wannan matsayin ’yan siyasar Abuja su mamaye ta ba.”

- Jamilu Muhammed

Jamilu Muhammed ya bayyana cewa an yanke hukuncin dakatar da su ne a wani taro na gaggawa da shugabanni da mambobin jam’iyyar na gaskiya suka gudanar, wadanda suka kasance masu biyayya ga jam’iyyar tun kafin shigowar 'yan siyasar Abuja.

Kara karanta wannan

Shekarau ya yi karatun ta natsu, ya gano hanyar kifar da Tinubu a 2027

Jam'iyyar ADC ta nada shugannin riko

Jam’iyyar ta nada Abdulrazaq Abubakar Isah Iko a matsayin shugaban riko, yayin da Adamu Aliyu zai rike mukamin sakataren ADC na jihar har zuwa lokacin da za a gudanar da sabon zaben shugabanni, rahoton The Sun ya tabbatar da haka.

Rikici ya kunno kai a jam'iyyar ADC
ADC ta ladabtar da wasu shugabanninta a Kebbi Hoto: @atiku
Asali: Facebook

Jam'iyyar ADC a Kebbi ta gargadi wadanda aka dakatar da su da su daina gabatar da kansu a matsayin ’yan jam’iyyar, tare da daina shiga harkokin jama’a ko na kashin kai da sunan jam’iyyar.

Sun kuma yi Allah wadai da tarurrukan siyasa da mambobin kwamitin da aka dakatar ke gudanarwa, suna mai cewa kamfen a yanzu ya sabawa dokar zabe, don haka jam’iyyar ba ta yarda da shi ba.

Jam’iyyar ta bukaci INEC da sauran hukumomi masu ruwa da tsaki su dauki mataki kan masu karya doka.

ADC ta zargi EFCC da muzgunawa 'yan adawa

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar ADC ta nuna rashin gamsuwarta kan tsare tsohon gwamnan jihar Sokoto da hukumar EFCC ta yi.

Kara karanta wannan

2027: Peter Obi ya yi hangen nesa, ya gano hanyar kwace mulki a hannun APC

Jam'iyyar ADC ta yi zargin cewa hukumar EFCC ta zama karen farautar APC wajen muzgunawa 'yan hamayya.

ADC ta bayyana cewa hukumar EFCC tana tsangwamar 'yan adawa yayin da ko kadan ba ta bincikar mutanen da ke cikin jam'iyya mai mulki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng