PDP Ta Yi Wa Shugaba Tinubu Saukale, Ta Hango Makomarsa a Zaben 2027
- Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta taso shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a gaba kan salon mulkinsa
- PDP ta bayyana cewa Shugaba Tinubu ya zama baƙar haja a wajen ƴan Najeriya saboda yadda yake gudanar da mulkinsa
- Jam'iyyar PDP ta bayyana ƴan Najeriya marasa kishin ƙasa ne kawai za su sake zaɓar Shugaba Tinubu a zaɓen 2023
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Jam’iyyar adawa ta PDP ta sake caccakar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.
Jam'iyyar PDP ta bayyana Shugaba Tinubu a matsayin zaɓin da bai dace ba ga ƴan Najeriya yayin da ake tunkarar zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Asali: Twitter
Sakataren yaɗa labarai na ƙasa na PDP, Debo Olugunagba ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja a ranar Litinin, cewar rahoton jaridar The Punch.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Me PDP ta ce kan Shugaba Tinubu?
Ya bayyana cewa PDP ita ce kaɗai jam’iyya da ke da ƙarfin kayar da Shugaba Tinubu da kuma jam’iyyar APC.
"PDP ita ce kaɗai jam’iyyar da za ta iya sauke APC daga mulki. Muna da goyon baya, muna da jama’a, kuma mun samu karɓuwa a faɗin ƙasa baki ɗaya."
"Babu wata unguwa ko gari da babu ƴaƴan PDP, domin kuwa PDP jam’iyyar talakawa ce. Ƴan Najeriya na matuƙar fatan dawowar PDP kan mulki."
"La’akari da kura-kurai da gazawar APC da dama, zan iya cewa babu wani ɗan Najeriya mai kishin ƙasa, ko wata ƙungiya ko wata jam’iyya da za ta goyi bayan Tinubu a 2027."
"Gaskiya ne cewa Shugaba Bola Tinubu baƙar haja ce. Don haka babu wanda ke fuskantar wahalhalu irin waɗanda muke fuskanta da zai sake kaɗa ƙuri’a gare shi."
“Tinubu baƙar haja ce kuma shugaban ƙasa ne wanda zai yi wa’adin mulki ɗaya kacal."
- Debo Olugunagba

Asali: Twitter
PDP ba ta damu da masu ficewa ba
Game da sauya sheƙar wasu mambobinsu zuwa jam’iyyar APC da kuma sabuwar haɗaka ƙarƙashin tutar ADC, Ologunagba ya bayyana cewa:
“Jam’iyyarmu jam’iyya ce mai ƙarfi wacce ke da karɓuwa sosai. Abin da ya kamata a fahimta shi ne cewa mutanen da suka gina jam’iyyar ba su sauya sheƙa"
"Ba su sauya sheka saboda yunwa ko rashin tsaro ba."
"Mutanen da ke da rinjaye a jam’iyyarmu, da kuma ƴan Najeriya da ba su da ra’ayin wata jam’iyya, suna fatan ceto daga PDP. Don haka, ba su sauya sheka."
Gwamna Kefas ya musanta shirin barin PDP
A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya musanta jita-jitar da ke nuna yana shirin barin jam'iyyar PDP.
Gwamna Agbu Kefas ya bayyana cewa bai da wani shiri na shiga jam'iyyar haɗaka watau ADC wacce ke samun karɓuwa.
Ya bayyana cewa biyayyarsa ga PDP ba mai yankewa ba ce kuma bai da niyyar komawa wata jam'iyya.
Asali: Legit.ng