Gwamna Ya Fito Ya Yi Magana kan Shirinsa na Neman Zama Shugaban Ƙasa a 2027

Gwamna Ya Fito Ya Yi Magana kan Shirinsa na Neman Zama Shugaban Ƙasa a 2027

  • Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya yi ƙarin haske kan raɗe-raɗin yana shirin fitowa takarar shugaban kasa a 2027
  • A cewar gwamnan, yanzu ya maida hankali ne wajen kammala zangon mulki na biyu amma bai fara tunanin shugabancin kasa ba
  • Makinde ya bukaci ɗaliban da ke karatu a manyan makarantun gaba da sakandire na jihar Oyo su cike fom na neman lamunin karatu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Oyo - Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya ba da amsar tambayar da ake yawan yi masa kan burin takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Gwamna Makinde ya bayyana cewa a halin yanzu ya maida hankali ne kan kammala wa'adin zango na biyu da al'ummar jihar Oyo suka ba shi amana.

Gwamna Seyi Makinde
Gwamna Makinde ya ce hankalinsa na kan amanar da mutanen Oyo suka ɗora masa Hoto: @seyiamakinde
Asali: Twitter

Seyi Makinde ya yi wannan furucin ne a wata hira da manema labarai da safiyar ranar Asabar, 21 ga watan Disamba, 2024 a Ibadan, kuma ya wallafa bidiyon a Youtube.

Kara karanta wannan

Gwamna Radda ya ziyarci mutanen da aka ceto a hannun 'yan bindiga, ya ba da tallafi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Makinde zai nemi shugaban ƙasa?

Ya kara da cewa ya mayar da hankali ne wajen kammala wa’adinsa na biyu amma ko kaɗan bai fara tunanin tsayawa takara a zaben shugaban kasa na 2027 ba.

Gwamnan ya ce:

“Ina da aikin da al’ummar Jihar Oyo suka ba ni, don haka shi ne abin da na fi mayar da hankali a kai a yanzu, ba shugabancin kasa a 2027 ba."

Makinde ya yi alkawarin gina tituna

Yayin wannan tattaunawa da manema labarai, Makinde ya taɓo wasu ayyukan tituna da gwamnatinsa ke yi a faɗin jihar Oyo.

Ya yi wa al’ummar jihar Oyo alkawarin cewa gwamnatinsa za ta tabbatar da kammala dukkan hanyoyin da ta fara ginawa ko take gyarawa.

Makinde ya kuma amsa rokon wani ɗalibi na rage kudin makaranta, inda ya roƙi dalibai su cike neman lamunin karatun gwamnatin tarayya.

Gwamna Makinde ya soki kalaman Ganduje

A wani rahoton, an ji cewa Gwamna Seyi Makinde ya caccaki kalaman shugaban APC na ƙasa cewa sun shirya karɓe mulkin jihohin Oyo da Osun.

Makinde ya bayyana cewa ga dukkan alamu za su koyawa Abdullahi Ganduje darasin da bai taɓa gani ba a tsawon rayuwarsa a zaɓukan jihohin biyu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel