Babbar Kotu Ta Soke Matakin Majalisa, Ta Dawo da Ciyamomi 18 da Aka Dakatar

Babbar Kotu Ta Soke Matakin Majalisa, Ta Dawo da Ciyamomi 18 da Aka Dakatar

  • Kotun jihar Edo mai zama a Benin ta dawo da dakatattun ciyamomi da mataimakansu na kananan hukumomi 18
  • Wannan hukunci na zuwa ne kwanaki kalilan bayan Majalisar dokoki ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomin kan zargin almubazzaranci
  • Alkalin kotun, mai shari’a Efe Ikponmwonba ya umarci kowane ɓangare ya tsaya a matsayinsa, ya ɗage zaman zuwa watan Fabrairu, 2025

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Edo - Babbar kotun Edo mai zama a Benin City ta soke matakin da majalisar dokokin jihar ta ɗauka kan shugabannin ƙananan hukumomi 18.

Idan baku manta ba Majalisar dokokin jihar Edo ta dakatar da ciyamomi 18 da mataimakansu a faɗin kananan hukumomin jihar kan zargin almubazzaranci.

Gwamnan Edo, Monday Okpebholo.
Shugabannin ƙananan hukumomi 18 na Edo sum yi nasara a babbar kotun jihar Hoto: @M_Akpakomiza
Source: Twitter

Sai dai a zaman yau Juma'a, 20 ga watan Disamba, 2024 babbar kotun Edo ta soke wannan mataki na majalisa, kamar yadda Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Kotu ta yanke hukunci kan MTN, ta ci tararsa N15m kan cire kudi babu ka'ida

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotu ta maido ciyamomi 18 kan kujerunsu

Kotun ta ba da umarnin maida dukkan ciyamomin da mataimakansu kan kujerunsu har zuwa lokacin da za ta gama sauraron karar kuma ta yi hukunci.

Kotun karkashin jagorancin mai shari’a Efe Ikponmwonba ta ba da umarnin ne biyo bayan karar da ciyamomi da mataimakansu suka shigar gabanta.

Alkali ya takawa gwamnan Edo burki

Har ila yau umarnin kotun ya haka Gwamna Monday Okpebholo, gwamnatin Edo da sauran waɗanda ake tuhuma amfani da matsayar Majalisar dokoki.

Alkalin ya umarci kowane ɓangare su ci gaba da zama a yadda yake gabanin kotu ta gama da sauraron karar da aka shigar gabanta ranar 12 ga watan Disamba, 2024.

Daga nan ne alkalin mai shari’a Efe Ikponmwonba ya dage shari’ar zuwa ranar 17 ga Fabrairu, 2025, domin a ci gaba da sauraron ƙarar.

Bugu da ƙari, ya ba da umarnin a aika sammaci ga waɗanda ake tuhuma domin su san abin da ke faruwa kafin ranar zama na gaba.

Kara karanta wannan

Ribas: Babbar kotu ta tsige shugaban jam'iyyar APC da ƴan kwamitin NWC

EFCC ta gayyaci ciyamomin jihar Edo

A wani rahoton, kun ji cewa hukumar EFCC ta gayyaci shugabannin ƙananan hukumomin Edo zuwa ofishinta domin su amsa wasu tambayoyi.

A wata sanarwa da ta aikewa sakataren gwamnatin Edo, EFCC ta sanya wa ciyamomin ranakun da takon ganinau a ofishinta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262