A ƙarshe, Tinubu Ya Gwangwaje Kwankwaso, Bichi da Manyan Mukamai

A ƙarshe, Tinubu Ya Gwangwaje Kwankwaso, Bichi da Manyan Mukamai

  • Hon. Musa Ilyasu Kwankwaso ya samu muƙami a gwamnatin Bola Tinubu a yau Laraba 18 ga watan Disambar 2024
  • Tinubu ya amince da nadin Ilyasu Kwankwaso da Injiniya Rabi’u Sulaiman Bichi a hukumar raya kogunan Hadejia-Jama’are
  • Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadiminsa na musamman, Bayo Onanuga ya fitar a yau Laraba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi sababbin nade-nade a gwamnatinsa a yau Laraba 18 ga watan Disambar 2024.

Tinubu ya amince da nadin sababbin shugabanni a hukumomin raya kogunan da ke karkashin ma’aikatar Ruwa ta Tarayyar Najeriya.

Musa Ilyasu Kwankwaso ya samu muƙami a gwamnatin Tinubu
Shugaban kasa, Bola Tinubu ya ba Musa Ilyasu Kwankwaso mukami a gwamnatinsa. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Musa Ilyasu Kwankwaso.
Source: Facebook

Tinubu ya ba Musa Ilyasu Kwankwaso mukami

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Bayo Onanuga ya fitar a shafinsa na Facebook a yau Laraba 18 Disambar 2024.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya tafi hutu bayan gabatar da kasafin kudin 2025

Sanarwar ta ce an nada Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso, Daraktan Gudanarwar Kuɗi a Hukumar Raya Kogunan Hadejia-Jama’are da ke kula da Kano, Jigawa da Bauchi.

Daga cikin sababbin nade-naden, an tabbatar da Injiniya, Rabi’u Sulaiman Bichi a matsayin Babban Darakta na hukumar.

Ga cikakken jerin sunayen waɗanda aka nada:

Hukumar Raya Kogunan Hadejia-Jama’are (Kano, Jigawa da Bauchi)

1. Mamman Da’u Aliyu – Shugaban Hukuma (Jigawa)

2. Engr. Rabiu Suleiman Bichi – Babban Darakta (Kano)

3. Tijjani Musa Isa – Daraktan Gudanarwa, Shirye-shirye da Tsarawa (Jigawa)

4. Hajiya Zainab Gamawa – Daraktar Gudanarwa, Ayyukan Noma (Bauchi)

5. Baffa Dandatti Abdulkadir – Daraktan Gudanarwa, Injiniya (Kano)

6. Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso – Daraktan Gudanarwa, Kuɗi (Kano).

Tinubu ya ba Bwala Daniel muƙami

Mun ba ku labarin cewa, Shugaba Bola Tinubu ya ba tsohon hadimin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar mukami a gwamnatinsa.

Kara karanta wannan

Muhimman abubuwan da yamata ku sani game da kasafin kudin 2025

Mr. Daniel Bwala ya samu muƙamin ne a gwamnatin Bola Tinubu a ranar Alhamis 14 ga watan Nuwambar 2024 bayan ya dawo jam'iyyar APC.

Tinubu ya amince da nadin Bwala a matsayin hadiminsa na musamman a bangaren sadarwa da hulda da jama'a.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.