Gwamnonin PDP sun Shiga Ganawa a Jos, Sun Jero Tsare Tsaren Kawo Sauyi a Kasa

Gwamnonin PDP sun Shiga Ganawa a Jos, Sun Jero Tsare Tsaren Kawo Sauyi a Kasa

  • Yayin da suke kokarin kawo sauyi kan yadda jam'iyyar ke tafiya, gwamnonin PDP suna ganawa ta musamman a jihar Plateau
  • Gwamnonin sun taru ne domin nemo hanyoyin kawo hadin kai da zaman lafiya a jam'iyyar tare da dawo da martabarta
  • Yayin taron, gwamnoni sun bukaci Bola Tinubu ya yi gaggawar shawo kan matsalolin da ake fama da su musamman duba da tsare-tsarensa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Plateau - Kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP sun shiga ganawa kan wasu matsaloli a jihar Plateau da ke Arewacin Najeriya.

Gwamnonin karkashin PDP suna ganawar domin shawo kan matsalolin jam'iyyar da kuma cigaban ƙasa.

Gwamnonin PDP na ganawa a jihar Plateau
Gwamnonin jam'iyyar PDP sun shiga ganawa ta musamman a jihar Plateau. Hoto: Peoples Democratic Party.
Source: Facebook

PDP ta yi alkawarin kawo sauyi a kasa

Mai masaukin baki, Gwamna Caleb Mutfwang ya tabbatar da himmatuwarsu wurin kawo hadin kai a jam'iyyar, cewar Leadership.

Kara karanta wannan

Gwamnoni sun taso shugaban PDP na ƙasa da NWC a gaba kan Taron NEC

Mutfwang ya kuma ba da tabbacin dawo da martabar jam'iyyar a idon yan Najeriya kamar yadda take a baya.

Gwamnan ya nuna farin cikinsa da yadda gwamnonin PDP da kuma masu ruwa da tsakin jam'iyyar suka cika a jihar domin wannan taro.

Gwamna Mutfwang ya godewa gwamnonin PDP

"Duk da wannan taro musamman an shirya ne domin gwamnoni, amma abin farin ciki ne yadda jiga-jigan jam'iyyar suka cika wannan taro domin ba gwamnonin goyon baya."
"Jam'iyyar PDP ba iya zakulo hanyoyin kawo zaman lafiya a cikinta za ta yi ba har da dawo da martabar jam'iyyar a idon yan Najeriya."

Caleb Mutfwang

Gwamnonin sun yi Allah wadai da tsare-tsaren Bola Tinubu inda suka bukaci ya janye wasu tsare-tsare masu tsauri domin saukakawa yan kasa.

Daga bisani, Gwamna Mutfwang ya bayyana tasirin Plateau a bunkasa jam'iyyar tun farkon kafa ta inda ya jihar gidan PDP ce, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Ana zargin alaka ta yi tsami tsakanin Namadi da Badaru, Gwamna ya magantu

Gwamnonin Najeriya sun gana a Abuja

A baya, kun ji cewa kwana daya bayan Shugaba Bola Tinubu ya turawa shugabannin Arewa sako, kungiyar gwamnonin Najeriya ta shiga ganawar gaggawa.

Gwamnonin ƙarƙashin jagorancin Gwamna AbdulRahman AbdulRazak na Kwara za su tattauna matsaloli da dama da suka shafi Najeriya.

Daga cikin abubuwan da ake sa ran za su tattauna akwai asusun rarar danyen mai (ECA) da harajin man fetur da sauran abubuwa muhimmai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.