Gwamnoni Sun Yi wa 'Yan Majalisa Barazanar Rasa Takarar 2027 kan Kudirin Harajin Tinubu

Gwamnoni Sun Yi wa 'Yan Majalisa Barazanar Rasa Takarar 2027 kan Kudirin Harajin Tinubu

  • Sabani tsakanin gwamnoni da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan kudirin haraji na kara girma, an fara yi wa yan majalisa barazana
  • Jami'in yada labaran majalisar dokokin Najeriya ya bayyana cewa yan majalisa sun fara fuskantar barazana daga gwamnonin jihohinsu
  • Tun a karon farko dai gwamnoni suka ki yarda da kudirin gyaran harajin amma shugaba Bola Tinubu ya dage kan tabbatar da shi

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Ana cigaba da takaddama kan kudirin haraji da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya aika majalisa.

Rahotanni na nuni da cewa gwamnoni sun fito da hanyar da za su yaki kudirin a majalisun Najeriya.

Majalisa
An yi wa yan majalisa barazana kan kudirin haraji. Hoto: House of Representatives, Federal Republic of Nigeria
Source: Facebook

Punch ta wallafa cewa mataimakin mai magana da yawun majalisar dokoki, Hon. Philip Agbese ya ce suna fuskantar barazana daga gwamnoni.

Kara karanta wannan

Bello Turji da mayakansa na shan luguden wutan kwanaki 4 a jere

Gwamnoni na barazana ga yan majalisa

The Sun ta wallafa cewa sakamakon dagewa da shugaba Bola Tinubu ya yi kan gabatar da kudirin haraji ga majalisa, gwamnoni sun fito da wata barazana.

Mataimakin mai magana da yawun majalisa, Philip Agbese ya ce an fara barazanar hana tikitin takara ga duk wanda ya amince da kudirin.

Tun a ranar 3 ga Satumban 2024 ne shugaban kasa ya tura kudirin gyara dokokin haraji ga majalisar ƙasa.

"Gwamnoni sun fara barazanar hana tikitin takara a 2027 ga duk wanda ya amince da kudirin haraji na Bola Tinubu.
Sai dai matukar muna majalisa, ba abin da zai hana mu goyon bayan shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen ceto tattalin Najeriya.
Dukkan yan jam'iyyu mun hada kai domin ganin Najeriya ta cigaba, kuma wannan shi ne fatan shugaban majalisa."

- Philip Agbese

Ana sa ran cewa a yau Litinin yan majalisar za su yi zama kan kudirin harajin kafin dawowa aiki a ranar Talata.

Kara karanta wannan

"Mun bar shi da halinsa:" Gwamnatin Tinubu za ta daina tankawa Atiku

Gwamnoni sun yi magana kan tsarin haraji

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnan Nasarawa, Abdullahi Sule ya sake magana kan kudirin haraji da ya jawo ce-ce-ku-ce tsakaninsu da Bola Tinubu.

Gwamna Abdullahi Sule ya ce gwamnonin Arewa ba su yin adawa da sauya fasalin haraji a Najeriya kawai suna bukatar a yi gyara ne.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng