APC Ta Rikice da Sarakunan Gargajiya Suka Yi Murabus, Sun bi Layin Sanata

APC Ta Rikice da Sarakunan Gargajiya Suka Yi Murabus, Sun bi Layin Sanata

  • Yayin da rigimar jam'iyyar APC ke kara ƙamari a jihar Sokoto, wasu sarakunan gargajiya sun yi murabus daga sarauta
  • Sarakunan gargajiya sun fito ne daga yankin Sokoto da Gabas inda Sanata Ibrahim Lamido ke wakilta a Majalisar Tarayya
  • Hakan ya biyo bayan samun matsala tsakanin sanatan da shugabannin jam'iyyar APC a jihar kan rashin tsari

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Sokoto - Wasu sarakunan gargajiya a Sokoto ta Gabas sun yi murabus daga sarautar da suke rike da su.

Gamayyar sarakunan sun dauki wannan mataki ne domin bin Sanata Ibrahim Lamido ana tsaka da rigimar APC.

Sarakunan gargajiya sun yi murabus saboda rigimar APC
Rigimar APC ta yi tsami da wasu sarakunan gargajiya suka yi murabus a Sokoto. Hoto: Ibrahim Lamido, Aliyu Magatakarda Wamakko.
Asali: Facebook

Sokoto : Sarakuna sun yi watsi da gwamna

Kara karanta wannan

Rigima ta kauren tsakanin wasu sarakuna kan yankunan da suke mulki a Najeriya

Sarakunan gargajiya sun bayyana haka ne a yau Lahadi 27 ga watan Oktoban 2024 a Sokoto, cewar rahoton Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sarakunan sun nuna goyon bayansu ga sanatan da ke wakiltar Sokoto ta Gabas da ke da matsala da shugabannin APC.

Suka ce sun dauki matakin tube rayukansu ne da bin sanatan kan korarin dakile matsalar tsaro a yankunansu.

Wasu daga sarakunan da suka yi murabus

Daga cikin wadanda suka ajiye rawunan nasu akwai Ubandoman Gatawa da Danmalan Ubandawaki da Salihu Katukan Gobir da Isah Haruna da Dangaladima Bashar.

Sai kuma Hassan S Fada da Yakubu Maigari da Malam Haruna da dagacin kauyen Kumbuli, Alhaji Ibrahim Gatawa da Mu’azu Mohammed Gatawa da sauran sarakunan masu yawa.

"Kowa ya sani Sanata Lamido ya kawo yan sa kai na CJTF kamar yadda aka yi a Maiduguri domin yakar yan bindiga a Isa da Sabon Birni."

Kara karanta wannan

Yan majalisa sun amince da shirin karya farashin abinci

"Tabbas ana cigaba da samun nasarori kan yaki da ta'addanci yayin da al'umma ke rayuwa cikin salama."

- Cewar sanarwar

Rigimar APC ta sake daukar sabon salo a Sokoto

Kun ji cewa rikicin cikin gida na jam'iyyar APC a jihar Sokoto ya sake dagulewa kan wanda zai jagorance ta.

Jam'iyyar ta dade da rabewa gida biyu inda aka raba tafiya tsakanin Sanata Aliyu Wamakko da Samata Ibrahim Lamido.

Hakan ya biyo bayan zargin Sanata Wamakko da cin hanci da wasu yan jam'iyyar ke cewa yana bata musu suna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.