Kwankwaso Ya Gana da Ƴan Majalisar Tarayya na NNPP, An Nemi Mutum 3 An Rasa

Kwankwaso Ya Gana da Ƴan Majalisar Tarayya na NNPP, An Nemi Mutum 3 An Rasa

  • Jagoran NNPP na ƙasa, Rabiu Musa Kwankwaso ya gana da ƴan majalisar tarayya na jam'iyyar a gidansa da ke Abuja
  • Rahotanni sun bayyana cewa ƴan majalisa uku sun kauracewa zaman, wanda ana ganin hakan na da alaƙa da rikicin da ya ɓarke a NNPP
  • Sanata Kawu Sumaila na cikin waɗanda suka ki halartar taron saboda zargin ana nuna masu wariya wajen tafiyar da harkokin NNPP

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Jagoran Kwankwasiyya, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya gana da ƴan majaisar tarayya na jam'iyyar NNPP a jihar Kano.

Wannan ganawa na zuwa ne a daidai lokacin da jam'iyyar ke fama da rikicin ciki wanda ya raba kawunan wasu daga cikin kusoshin NNPP.

Kara karanta wannan

Tsohuwar Minista ta taimaka wajen samo $57.5bn domin kafa Biafara? Gaskiya ta fito

Kwankwasonda ƴan majalisar NNPP.
Ganawar Kwankwaso da ƴan majalisar NNPP ya kara nuna akwai baraka a jam'iyyar Hoto: @SaifullahiHon
Asali: Twitter

Hadimin Kwankwaso na fannin kafafen sada zumunta, Saifullahi Hassan ya wallafa hotunan ganawar jagoran NNPP na ƙasa da ƴan majalisar a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taron wanda aka gudanar a gidan Kwankwaso na Abuja, an yi shi ne don magance rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar NNPP reshen Kano.

Ƴan majalisa 3 sun kauracewa zama da Kwankwaso

Sai dai ba a ga fuskokin mutum uku daga cikin ƴan majalisar a wurin taron ba, Sanata Suleiman Kawu Sumaila, Hon. Kabiru Alhassan Rurum, da Aliyu Sani Madakin Gini

Rashin ganin fuskokin kusoshin uku ya kara tabbatar da raɗe-raɗin da ake yaɗawa cewa akwai tsama a jam'iyyar NNPP.

An tattaro cewa Aliyi Madakin Gini ya daina sa jar hula, alamar ƴan Kwankwasiyya, sannan ba a gan shi a wurin muhimman tarukan NNPP ba.

Kara karanta wannan

Jerin ministocin da Tinubu ya kora daga aiki da jihohin da suka fito a Najeriya

NNPP na fama da rikicin cikin gida

Rurum da Sanata Kawu Sumaila sun nuna ɓacin ransu kan yadda Kwankwaso ya maida su saniyar ware wajen fitar da ƴan takarar ciyaman da kansiloli a Kano.

Wannan ƙorafin ya sa aka fara tunanin suna shirin sauya sheka daga NNPP musamman ma saboda saɓanin da ka samu kan dokar masarautar Kano.

Rashin halartar wadannan ‘yan majalisar ya fara tayar da kura a tsakanin magoya bayan jam’iyyar.

Sauran ‘yan jam’iyyar NNPP daga Kano, irin su Sanata Rufa’i Sani Hanga da Tijjani Abdulqadir Jobe, sun halarci zaman a Abuja.

Kwankwaso ya yi magana kan ilimi

A wani rahoton kuma tsohon gwamnan Kano, Rabiu Kwankwaso ya ce gudummawar da ya bayar a ɓangaren ilimi na gina jami'o'i biyu na faranta masa rai.

Jagoran NNPP ya bayyana cewa a dukkan ayyukan da ya yi lokacin yana matsayin gwamnan Kano, ya fi jin daɗin gina jami'o'in nan

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262