Kotu Ta Jiƙawa Jam'iyyar NNPP Aiki Awanni Kafin Zaben Kananan Hukumomi a Ƙano

Kotu Ta Jiƙawa Jam'iyyar NNPP Aiki Awanni Kafin Zaben Kananan Hukumomi a Ƙano

Kano - Yayin da ake shirye-shiryen zaɓen kananan hukumomi a gobe Asabar a Kano, babbar kotun tarayya ta kori ƴan takarar NNPP 44.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Kotun wanda ke zamanta a Kano ta kori dukkan ƴan takarar ciyaman na jam'iyyar NNPP a zaɓen da aka shirya yi ranar Asabar, 26 ga watan Oktoba, 2024.

Abba a wurin taron NNPP.
Kotu ta soke tikicin ƴan takarar ciyaman na NNPP a zaben kananan hukumomin Kano Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Mai shari'a Simon Amobeda ne ya yanke wannan hukunci ranar Jumu'a a ƙarar da Injiniya Muhammad Babayo da tsagin NNPP suka shigar, Channels tv ta kawo.

Mai Shari'a Amobeda ya umarci hukumar zaɓen Kano (KANSIEC) ta karbi sabon sunayen ƴan takarar ciyaman daga tsagin NNPP da Dalhatu Shehu Usman ke jagoranta.

Alkalin ya ce dole ne hukumar KANSIEC ta amince da jerin sunayen ‘yan takarar da masu kara suka gabatar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Kotu ta yanke hukunci kasa da awanni 24 kafin zaben Ciyamomi a jihar Kano

Ƙarar ta ƙunshi hukumar zabe ta ƙasa (INEC), KANSIEC, Sufeto Janar na ‘yan sanda, da daraktan hukumar DSS a matsayin wadanda ake tuhuma na 1, 2, 3 da 4.

"Kotu na umartar INEC da ka da ta ba hukumar zaɓen Kano kayan zaɓe domin gudanar da zaɓen da aka tsara ranar 26 ga watan Oktoba, 2024," in ji alkali.

Kotun ta kuma hana jami’an tsaro bayar da kariya a rumfunan zabe idan zaben ya gudana ba tare da sabunta jerin sunayen ‘yan takara ba.

Ku saurari ƙarin bayani...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: