Kaduna: APC Ta Lallasa PDP da Sauran Jam'iyyun Adawa a Zaben Ciyamomi
- Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kaduna (KAD-SIECOM) ta sanar da zaɓen shugabannin ƙananana hukumomin da aka gudanar a ranar Asabar
- Shugabar hukumar zaɓen ta bayyana cewa jam'iyyar APC mai mulki a jihar Kaduna ta lashe dukkanin kujerun ciyamomi 23 a zaɓen
- Hajara Mohammed ta kuma sanar da cewa APC ta lashe kujerun kansiloli 255 a zaɓen wanda jam'iyyun siyasa takwas suka fafata
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Kaduna - Jam’iyyar APC ta lashe zaɓe a dukkanin kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 23 na jihar Kaduna.
Jam'iyyar APC ta kuma lashe kujerun kansiloli 255 a zaɓen ƙananan hukumomin da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kaduna (KAD-SIECOM) ta gudanar ranar Asabar.
Tashar Channels tv ta ce shugabar hukumar zaɓen jihar, Hajara Mohammed, ce ta sanar da sakamakon zaɓen a ranar Asabar, 19 ga watan Oktoban 2024.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
APC ta lallasa ƴan adawa a Kaduna
Hajara Mohammed ta ce jam'iyyun siyasa takwas ne suka fafata a zaɓen, inda APC ta samu kujerun ciyamomi 23 da na kansiloli 255, rahoton jaridar Daily Trust ya tabbatar.
Ta ƙara da cewa jam’iyyar APC mai mulki ta samu nasara a ƙananan hukumomin da suka haɗa da Birnin-Gwari, Chikun, Igabi, Ikara, Jaba, Jema’a, Kachia, Kaduna ta Arewa da Kaduna ta Kudu.
Sauran ƙananan hukumomin da jam’iyyar APC ta lashe a cewar shugabar hukumar zaɓen sun haɗa da Kagarko, Kajuru, Kaura, Kauru, Kubau, Kudan, Lere, Makarfi, Sabon Gari, Sanga, Soba, Zango-Kataf da Zaria.
A ranar Asabar, 19 ga watan Oktoba ne dai aka gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin jihar Kaduna.
Mutane sun yi biris da doka a Kaduna
A wani labarin kuma, kun ji cewa mutanen Kaduna a ranar Asabar sun bijirewa dokar hana zirga-zirga da gwamnatin jihar ta sanya a faɗin jihar.
Gwamnatin jihar ta sanya dokar hana zirga-zirgar ne domin zaɓen ƙananan hukumomin jihar na ranar Asabar, 19 ga watan Oktoban 2024.
Asali: Legit.ng