Kaduna: APC Ta Lallasa PDP da Sauran Jam'iyyun Adawa a Zaben Ciyamomi

Kaduna: APC Ta Lallasa PDP da Sauran Jam'iyyun Adawa a Zaben Ciyamomi

  • Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kaduna (KAD-SIECOM) ta sanar da zaɓen shugabannin ƙananana hukumomin da aka gudanar a ranar Asabar
  • Shugabar hukumar zaɓen ta bayyana cewa jam'iyyar APC mai mulki a jihar Kaduna ta lashe dukkanin kujerun ciyamomi 23 a zaɓen
  • Hajara Mohammed ta kuma sanar da cewa APC ta lashe kujerun kansiloli 255 a zaɓen wanda jam'iyyun siyasa takwas suka fafata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kaduna - Jam’iyyar APC ta lashe zaɓe a dukkanin kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 23 na jihar Kaduna.

Jam'iyyar APC ta kuma lashe kujerun kansiloli 255 a zaɓen ƙananan hukumomin da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kaduna (KAD-SIECOM) ta gudanar ranar Asabar.

Kara karanta wannan

Jerin jihohin 3 inda APC da PDP za su fafata a zaben yau

APC ta lashe zaben ciyamomi a Kaduna
Jam'iyyar APC ta lashe zaben ciyamomi a Kaduna Hoto: @ubasanius
Asali: Twitter

Tashar Channels tv ta ce shugabar hukumar zaɓen jihar, Hajara Mohammed, ce ta sanar da sakamakon zaɓen a ranar Asabar, 19 ga watan Oktoban 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

APC ta lallasa ƴan adawa a Kaduna

Hajara Mohammed ta ce jam'iyyun siyasa takwas ne suka fafata a zaɓen, inda APC ta samu kujerun ciyamomi 23 da na kansiloli 255, rahoton jaridar Daily Trust ya tabbatar.

Ta ƙara da cewa jam’iyyar APC mai mulki ta samu nasara a ƙananan hukumomin da suka haɗa da Birnin-Gwari, Chikun, Igabi, Ikara, Jaba, Jema’a, Kachia, Kaduna ta Arewa da Kaduna ta Kudu.

Sauran ƙananan hukumomin da jam’iyyar APC ta lashe a cewar shugabar hukumar zaɓen sun haɗa da Kagarko, Kajuru, Kaura, Kauru, Kubau, Kudan, Lere, Makarfi, Sabon Gari, Sanga, Soba, Zango-Kataf da Zaria.

A ranar Asabar, 19 ga watan Oktoba ne dai aka gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin jihar Kaduna.

Kara karanta wannan

NNPP: Jam'iyyar Kwankwaso ta buɗe ƙofa, za a yi wa Tinubu taron dangi a 2027

Mutane sun yi biris da doka a Kaduna

A wani labarin kuma, kun ji cewa mutanen Kaduna a ranar Asabar sun bijirewa dokar hana zirga-zirga da gwamnatin jihar ta sanya a faɗin jihar.

Gwamnatin jihar ta sanya dokar hana zirga-zirgar ne domin zaɓen ƙananan hukumomin jihar na ranar Asabar, 19 ga watan Oktoban 2024.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng