Jigon PDP Ya Bayyana Yadda Tinubu Ya Hana Shi Barin Najeriya

Jigon PDP Ya Bayyana Yadda Tinubu Ya Hana Shi Barin Najeriya

  • Cif Olabode George ya bayyana dalilinsa na ƙin barin Najeriya bayan shugaba Bola Tinubu ya lashe zaɓen shugaban ƙasa
  • Tsohon mataimakin na shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa ya bayyana cewa haƙurin da aka ba shi ne ya sanya ya canza shawara
  • Ya bayyana cewa da Bola Tinubu bai turo a ba shi haƙuri ba, da tuni ya fice daga cikin ƙasar nan yadda ya yi alƙawari

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Legas - Tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa, Cif Bode George, ya yi magana kan dalilinsa na ƙin barin Najeriya bayan Shugaba Bola Tinubu ya lashe zaɓe.

Bode George ya bayyana cewa da a ce Bola Tinubu bai turo shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajbiamila, ya lallashe shi ba, da tuni ya bar ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Jagororin APC sun ba 'yan Najeriya shawara kan gwamnatin Tinubu

Bode George ya fadi dalilin kin barin Najeriya
Bode George ya ce Tinubu ya ba shi hakuri ka da ya bar Najeriya Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Olabode George
Asali: Facebook

Tsohon mataimakin shugaban na jam'iyyar PDP ya bayyana hakan ne yayin wata hira da tashar talabijin ta Arise tv a ranar Laraba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Yadda Tinubu ya lallaɓe ni", Bode George

Bode George ya bayyana cewa zuwan da Femi Gbajabiamila ya yi wajensa ne ya sanya ya canza shawara kan aniyarsa ta barin Najeriya.

A watan Janairun 2022, bayan da Tinubu ya bayyana aniyarsa ta yin takarar shugaban ƙasa, Bode George ya yi barazanar ficewa daga Najeriya idan har ya ci zaɓe.

"A lokacin yaƙin neman zaɓe na faɗi hakan kuma da gaske na ke cewa idan har Bola Tinubu ya yi nasarar lashe zaɓe, zan bar ƙasar nan."
"Suna jin hakan, sai Tinubu ya turo shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa wanda ƙanina ne daga jihar Legas, Femi Gbajabiamila, domin ya ba ni baki."

Kara karanta wannan

2027: Tsohon gwamnan PDP ya shawarci Atiku ya hakura da takara, ya fadi dalili

"Ya zo ya ce mani maigidansa ya ce na kwantar da hankali na. Sun san sun yi mani laifi. Sun ce suna ba ni haƙuri."

- Bode George

Jagoran PDP ya jiƙawa Atiku aiki

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban PDP, Bode George ya ce dole Atiku Abubakar ya jira 2031 idan yana son sake neman zama shugaban ƙasa.

Cif Bode George ya bayyana cewa dole ne yankin Kudancin Najeriya ya ci gaba da mulkin ƙasar nan har zuwa shekarar 2031.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng