"Durkusawa Wada:" Gwamnan Ribas Ya Fadi Dalilin ba Wike Hakuri

"Durkusawa Wada:" Gwamnan Ribas Ya Fadi Dalilin ba Wike Hakuri

  • Siminalayi Fubara ya bayyana cewa sai da ya yi kokarin ganin an kaucewa tashin hankali a jiharsa ta hanyar tattaunawa da Nyesom Wike
  • Gwamnan ya ce ya roki tsohon Mai gidansa, Nyesom Wike da ya zubar da makamansa domin samun wanzuwar zaman lafiya a jihar
  • Amma a cewar Fubara, Wike bai karbi rokon da ya yi masa ba, yanzu haka ana fama da rikicin da ake zargin da sa hannun magoya bayan Wike

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Rivers - Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara ya roki Ministan Abuja kuma tsohon uban gidansa, Nyesom Wike kan samuwar zaman lafiya a jihar.

Kara karanta wannan

"Ba komai za ka yi nasara ba": Gwamna ga minista, ya fadi silar rikici tsakaninsu

Gwamnan ya bayyana cewa sai da ya durkusa har kasa domin lallaba Nyesom Wike, wanda tsohon gwamnan Ribas ne kan dakatar da tashin hankali a jihar.

Fubara
Gwamnan Ribas ya fadi kokarinsa kan zaman lafiya a Ribas Hoto: Sir Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

A hira da ya yi da tashar Channels, Siminalayi Fubara ya bayyana dalilinsa na ba Nyesom Wike hakuri har ta kai ga durkusawa har kasa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wike: Gwamnan Ribas ya nemi sulhu

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa gwamnan jihar Ribas, Siminalyi Fubara ya bayyana cewa sai da ya yi kokarin a samu fahimtar juna tsakaninsa da Wike.

Gwamna Fubara ya ce ya yi haka ne domin a samu zaman lafiya mai dorewa a jihar, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba.

Gwamna Fubara ya gamsu da zaben Ribas

Gwamna Siminalayi Fubara ya bayyana gamsuwa kan yadda ya dage wajen tabbatar da gudanar da zabe a jiharsa duk da bijirewar magoya bayan Wike da yan jam'iyyarsa.

Kara karanta wannan

Gwamna ya fadi illar gobarar kasuwa ga Kano, Abba ya yi wa 'yan kasuwa alkawari

Ya bayyana cewa yanzu magana ake yi ta ci gaban al'umar jihar Ribas ba wasu tsirarun mutane ba, inda ya kara da cewa akwai bukatar kowa ya zubar da makamansa.

Tinubu ya yi gargadi kan rikicin Ribas

A baya mun ruwaito cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gargadi masu tayar da hankula bayan gudanar da zaben kananan hukumomi a jihar Ribas, ya nemi a dawo da doka da oda.

Gargadin shugaban na zuwa bayan an samu tashe tashen hankula da kone-kone da ya biyo bayan zaben kananan hukumomi da ya gudana a ranar Asabar duk da umarnin kotu na hana zaben.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.