AKISIEC: 'Yan Daba Sun Tafka Ta'asa, Sun Bankawa Ofishin Hukumar Zaɓe Wuta

AKISIEC: 'Yan Daba Sun Tafka Ta'asa, Sun Bankawa Ofishin Hukumar Zaɓe Wuta

  • Wasu miyagu sun banka wuta a ofishin hukumar zaɓe AKISIEC da ke garin Ibiatuk a ƙaramar hukumar Ibiono a jihar Akwa Ibom
  • Lamarin ya faru ne awanni kaɗan gabanin fara zaɓen kananan hukumomi yau Asabar, 5 ga watan Oktoba, 2025
  • Rundunar ƴan sanda ta tabbatar da kai harin amma ta ce bai hana zaɓe ba kuma miyagun ba su ci nasarar lalata kayayyakin zaɓe ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Akwa Ibom - Sa'o'i kaɗan gabanin fara zaɓen kananan hukumomi a jihar Akwa Ibom, an bankawa ofishin hukumar zaɓe mai zaman kanta wuta.

Rahotanni sun nuna wasu miyagu da ake zaton ƴan daban siyasa ne sun ƙona ofishin hukumar zaɓe ta jiha watau AKISIEC da ke Ibiatuk a ƙaramar hukumar Ibiono Ibom.

Kara karanta wannan

Jami'an tsaro sun kutsa daji sun sheke babban ɗan bindiga, sun ceto wani Sarki

Taswirar Akwa Ibom.
Yan daba sun ƙona ofishin hukumar zaɓe a Akwa Ibom Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Jami'ar hulɗa da jama'a ta rundunar ƴan sandan Akwa Ibom, ASP Timfon John ta tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, kamar yadda The Nation ta kawo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yan sanda sun yi bayanin abin da ya faru

Ta ce babu wanda ya mutu sakamakon banka wutar kuma dukkan kayayyakin zaɓe na nan lafiya, babu abin da ya same su.

Timfon John ta ce duk da ƙona ofishin hukumar zaɓen, jama'a sun fito rumfunan zaɓensu domin kaɗa kuri'a a zaɓen ciyamomi da kansiloli da ke gudana yau Asabar.

A cewarta, rundunar ‘yan sandan ta tura karin jami’an tsaro zuwa ofisoshin AKISIEC da ke fadin jihar Akwa Ibom domin dakile duk wani yunkurin tada zaune tsaye.

Yadda zaɓe ke tafiya a Akwa Ibom

An tattaro cewa a yau Asabar, 5 ga watan Oktoba, 2024, ake gudanar da zaɓen kananan hukumomi a Akwa Ibom.

Kara karanta wannan

Gwamna da mutane sun yiwa ƴan sanda ihu, sun kore su daga ofishin hukumar zabe

Bayanai sun nuna cewa babbar matsalar da aka fuskanta a zaɓen ita ce rashin isar kayayyaki da malaman zaɓe da wuri.

A rumfar zaɓe 001 da ke gunduma ta 14 a ƙaramar hukumar Uyo, har karfe 10:02 na safiya babu kayan zaɓe da malaman zaɓe, haka jami'an tsaro ma ba su je wurin ba.

Haka lamarin ya faru na rashin zuwan kayan zaɓen a Unit 2, Ward 11 a karamar hukumar Itu, kamar yadda Punch ta rahoto.

Zanga-zanga ta ɓarke a Rivers

A wani rahoton kuma magoya bayan ministan Abuja, Nyesom Wike sun fito kan tituna domin nuna adawarsu da zaɓen ƙananan hukumomin da ake yi a jihar Rivers.

Masu zanga-zangar sun buƙaci Gwamna Siminalayi Fubara da ya bi umarnin kotu wanda ya hana a gudanar da zaɓen a jihar

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262