Kwamacala: Gwamna Ya Nada 'Yarsa domin Maye Gurbin Matarsa a Ofishin 'First Lady'

Kwamacala: Gwamna Ya Nada 'Yarsa domin Maye Gurbin Matarsa a Ofishin 'First Lady'

  • Kwanaki bayan mutuwar matarsa, Gwamna ya gabatar da 'yarsa domin maye gurbin ayyukan ofishin marigayiyar
  • Gwamna Umo Eno ya tabbatar da nadin 'yarsa, Helen Eno domin zama a matsayin 'First Lady' na rikon kwarya
  • Hakan na zuwa ne bayan mutuwar matarsa, Mrs Patience Umo Eno kimanin kwanaki tara kenan da suka gabata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Akwa Ibom - Gwamna Umo Eno ya nada wacce za ta rike ofishin 'First Lady' bayan mutuwar matarsa.

Gwamna Eno ya tabbatar da nadin 'yarsa, Helen Eno domin rike ofishin marigayiyar, Patience Eno na rikon kwarya.

Gwamna ya maye gurbin matarsa da 'yarsa a matsayin 'First Lady'
Gwamna Umo Eno ya nada 'yarsa a matsayin 'First Lady' a Akwa Ibom. Hoto: Umo Eno, Mrs Patience Eno.
Asali: Twitter

Gwamna ya nada 'yarsa a ofishin matarsa

Kara karanta wannan

Bayan kwanaki 9 da mutuwar matarsa, Gwamna ya bude bakinsa, ya fadi halayen marigayiya

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ya fitar bayan ziyarar matar shugaban kasa, Remi Tinubu domin yi masa jaje, cewar rahoton Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Eno ya gabatar da 'yarsa, Helen inda ya ce za ta cigaba da ayyukan alheri da ofishin ya ke yi kafin mutuwar matarsa.

"Domin cigaba da ayyukan ofishin matar gwamna, ina gabatar muku da 'yata, Helen Eno saboda gudanar da ayyukan marigayiya."
"Helen za ta yi aiki kafada da kafada da mataimakin gwamna da kuma kwamishinar harkokin mata."

- Umo Eno

Eno ya bayyana kwarin guiwarsa kan kwarewar 'yar tasa inda ya ce yana da tabbacin za ta cigaba da ayyukan ofishin ba tare da matsala ba.

Matar Tinubu ta yaba da matakin gwamnan

A martaninta, Remi Tinubu da ta kai ziyara jihar domin jajantawa ta yaba da matakin da Gwamna Eno ya dauka.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Muhimman abubuwa 5 da Tinubu zai yi domin ceto kasa a halin kunci

Remi Tinubu ta ce hakan shi zai taimaka wurin cigaba da ayyukan da marigayiyar ta dauko domin mutunta ta.

Gwamna ya magantu bayan mutuwar matarsa

Kun ji cewa Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya yi magana kan rashin da ya yi na matarsa, Mrs Patience Eno.

Gwamnan ya fadi irin kewar matarsa da zai yi na tsawon rayuwarsa saboda irin gudunmawar da ta bayar a bangarori da dama.

Gwamnan ya yi godiya ga shugaba Bola Tinubu da yan jihar Akwa Ibom da sauran al'umma kan addu'o'in da suka yi mata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.