Bola Tinubu Ya Ji Matsin Lamba, Ya Canza Lambar Yabon da Ya Ba Shugaban Majalisa

Bola Tinubu Ya Ji Matsin Lamba, Ya Canza Lambar Yabon da Ya Ba Shugaban Majalisa

  • A ƙarshe shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sauya lambar girmamawar da ya ba kakakin majalisar wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas
  • Shugaba Tinubu ya karɓi kuskuren da ya yi a farko, ya ɗaga ƙimar Abbas zuwa lambar yabo ta GCON maimakon CFR da ya sanar a baya
  • Wannan na zuwa ne bayan ƴan majalisar wakilai sun yi fatali da CFR da Tinubu ya ba Abbas, inda suka nemi ya karrama shi da lamba mafi girma

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya karɓi koken ƴan majalisar wakilan tarayya, ya sauya lambar yabon da ya ba Rt. Hon. Tajudeen Abbas.

Bola Tinubu ya karrama kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas da lambar girma ta GCON maimakon CFR da ya ba shi a baya.

Kara karanta wannan

Kungiya ta fadawa Tinubu ribar da zai samu idan ya sasanta rikicin masarautar Kano

Bola Ahmed Tinubu da Tajudeen Abbas.
Shugaba Tinubu ya karɓi kuskurensa, ya karrama kakakin majalisar wakilai da lambar yabon GCON Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Tajudeen Abbas
Asali: Facebook

Yadda majalisa wakilai ta fusata a farko

Idan baku manta ba a jawabinsa na ranar 1 ga watan Oktoba, Tinubu ya sanar da karrama kakakin majalisar wakilai da mataimakin shugaban majalisar dattawa da lambar yabon CFR.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai hakan ya haifar da zazzafar mahawara a zauren majalisar wakilai, inda suka yi fatali da CFR da aka ba Abbas kuma suka nemi a ba shi lambar yabo mafi girma.

Mai taimakawa shugaban ƙasa kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga ya ce Tinubu ya gamsu da matsayar ƴan majalisar kuma ya gyara kuskuren da ya yi.

Bola Tinubu ya ba Tajudeen Abbas GCON

A sanarwar da ya wallafa a shafinsa na X yau Juma'a, Onanuga ya ce Shugaban Ƙasa Tinubu ya ɗaga darajar Rt Hon. Tajudeen zuwa GCON maimakon CFR.

Kara karanta wannan

'An kai mutumin da ya nemi Tinubu ya sauka daga mulki asibitin masu tabin hankali

"Shugaba Tinubu ya gamsu da koken ƴan majalisar wakilai kuma ya amince da gyara kurkuren da ya yi.
"Sakamakon haka shugaban ƙasar ya ɗaga darajar kakakin majalisar wakilai, ya ba shi lambar girma ta GCON maimakon CFR kamar yadda doka ta tanada.
"Nan ba da jimawa ba za a karrama shugaban majalisar dattawa, kakakin majalisar wakilai da sauran jagororin majalisa da shugabar alƙalai da lambobin yabon da aka ba su a hukumance."

- Bayo Onanuga.

Tinubu na shirin sake fasalin haraji

Kuna da labarin cewa a ranar Alhamis, kakakin majalisar wakilai, Abbas Tajudeen ya karanta wata wasika da shugaban kasa Bola Tinubu ya aiko masu

A cikin wasikar, Tinubu ya gabatarwa majalisar kudurori hudu da suka shafi sake fasalin haraji inda ya bukaci amincewarsu da gaggawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262