Dan Jam'iyyar PDP Ya Sauya Sheka Zuwa APC a Zauren Majalisar Tarayya

Dan Jam'iyyar PDP Ya Sauya Sheka Zuwa APC a Zauren Majalisar Tarayya

  • Jam'iyyar PDP mai adawa a ƙasar nan ta rasa ɗaya daga cikin ƴan majalisun da take da su a majalisar wakilan Najeriya
  • Ɗan majalisa mai wakiltar Ukwa ta Gabas/Ukwa ta Yamma daga jihar Abia, Chris Nkwonta ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC
  • Bayan sauya sheƙarsa zuwa APC, shugaban majalisar ya naɗa shi a matsayin shugaban wani kwamiti

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ɗan majalisar wakilai, Chris Nkwonta ya sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa jam'iyyar APC mai rinjaye.

Shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, ya sanar da sauya sheƙar Chris Nkwonta a zauren majalisar a ranar Laraba.

Dan majalisar PDP ya koma APC
Dan majalisar PDP daga Abia ya koma APC Hoto: @Imranmuhdz, @FrancisAdeboye
Asali: Twitter

Ɗan majalisar PDP ya koma APC

Chris Nkwonta yana wakiltar mazabar tarayya ta Ukwa ta Gabas/Ukwa ta Yamma daga jihar Abia, cewar rahoton jaridar The Cable

Kara karanta wannan

Jam'iyyar PDP ta yi nasara kan APC ana shirin zaben gwamna

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mambobin jam'iyyar APC a majalisar sun nuna farin cikinsu bayan sanarwar da aka yi na sauya sheƙarsa zuwa APC.

Ƴan adawa suna rashin amincewarsu

Sai dai, mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar, Aliyu Madaki, ya nuna rashin amincewarsa da sauya sheƙar.

Da yake kafa hujja da sashe na 68 na kundin tsarin mulkin ƙasar nan, Aliyu Madaki ya ce ɗan majalisa zai iya ficewa ne kawai daga jam’iyyar da ta ɗauki nauyin zaɓensa idan aka samu rikici a jam’iyyar.

Sai dai, shugaban majalisar ya yi watsi da batun na sa, inda ya ce akwai rikici a PDP, rahoton jaridar Independent ya tabbatar.

"Bayanan da nake da su sun nuna akwai wani ɓangare a PDP."

- Tajudeen Abbas

Daga bisani shugaban majalisar ya ayyana Chris Nkwonta a matsayin shugaban kwamitin majalisar kan hukumar ci gaban yankin Kudu maso Gabas.

Kara karanta wannan

Zaben Ondo: Ganduje da APC sun gamu da cikas ana dab da zabe

Mambobin APC sun koma PDP

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam’iyyar PDP a jihar Ondo ta karɓi masu sauya sheƙa daga APC a ranar Litinin, 30 ga watan Satumban 2024.

Jam’iyyar PDP ta yi maraba da tsohon shugaban hukumar raya yankin Neja-Delta, Dakta Benson Enikuomehin, tare da magoya bayansa sama da 200 zuwa cikin ta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng