"Na Shirya Rantsewa da Alƙur'ani Ban Taɓa Satar ko Kwabo ba," Tsohon Gwamnan El Rufai

"Na Shirya Rantsewa da Alƙur'ani Ban Taɓa Satar ko Kwabo ba," Tsohon Gwamnan El Rufai

  • Malam Nasiru El-Rufai ya ƙalubalanci tsofaffin gwamnonin Kaduna da sauran shugabanni, ya ce ya shirya rantsewa da Al'kur'ani bai saci ko kwabo ba
  • Tsohon gwamnan ya ce bai shiga harkar siyasa domin neman kudi ba, ya shiga ne domin yi wa al'umma aiki
  • Majalisar dokokin Kaduna tana zargin gwamnatin El-Rufai da yin sama da fadi da N423bn a shekaru takwas

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna - Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce ya shiga siyasa ne don ya yiwa jama’a hidima, ba don neman kudi ko satar dukiyar talakawa ba.

Malam El-Rufai ya ƙara da cewa ya gamsu da abubuwan da ya yi a siyasa tun kafin ya zama gwamnan jihar Kaduna a 2015.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Ana murnar samun ƴanci, gwamna ya ƴanta fursunoni a Najeriya

Malam Nasiru El-Rufai.
Malam Nasiru El-Rufai ya ce a shirye yake ya rantse da Alkur'ani bai taba satar ko kwandala a Kaduna ba Hoto: Nasir El-Rufai
Asali: Twitter

Ya bayyana haka ne a wani shirin Hausa da aka watsa a gidan rediyon Freedom da ke Kaduna a safiyar ranar Talata, 1 ga watan Oktob, Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majalisar Kaduna na zargin gwamnatin El-Rufai

Idan baku manta ba majalisar dokokin jihar Kaduna na zargin gwamnatin El-Rufai da karkatar da sama da Naira biliyan 423 cikin shekaru takwas da ya yi yana mulki.

Tsohon gwamnan da sauran abokan aikinsa sun musanta zarge-zargen satar kuɗin al'umma, inda suka ce gwamnatin jihar da majalisa na masu bi-ta da ƙulli.

Da yake jawabi a shirin, El-Rufai ya ce a shirye yake ya rantse da Alƙur’ani a duk lokacin da tsofaffin gwamnonin Kaduna da shugabannin yanzu suka rantse ba su saci ko sisi ba.

"Na shirya ratsewa da Alƙur'ani," El-Rufai

"Na yi shiru ne don naga yadda abubuwan za su kasance, amma ni dai ina ƙara godewa Allah da rokonsa ya taimake ni saboda ni ɗan adam ne, a koda yaushe ina kokarin kaucewa aikata laifi ko cin amanar jama'a.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Gwamna ya lissafo ni'imomi 3 a kasar nan, ya nemi a dage da addu'a

"Ina yawan faɗa idan har tsofaffin gwamnonin Kaduna da sauran shugabanni za su rantse da Alƙur'ani ba su taba ɗaukar kuɗin al'umma ba, nima a shirye nake na rantse.
"Saboda na san ban shiga siyasa don na saci kuɗin jama'a ba, na shiga siyasa ne domin na yiwa al'ummar Kaduna aiki, ba kuɗi na zo nema ba, ina ƙara gode Allah, na gamsu da abubuwan da na yi tun kafin zama gwanna.

- Malam Nasiru El-Rufai.

Tsohon gwamnan ya ƙara da cewa a yanzu ana zarginsa na karkatar da wasu kuɗafe ba tare da faɗin a ina kudin suka ɓata ko wanda ya sace su ba.

Uba Sani ya musanta raba gari da El-Rufai

A wani labarin kuma gwamnan Kaduna, Uba Sani ya musanta rade-radin da ake yadawa cewa ya na yiwa tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai bi-ta-da-kulli.

Uba Sani ya ce tun 1999 ya ke da alaka mai kyau da dukkanin tsofaffin gwamnonin jihar kuma bai ware Malam Nasir El-Rufai ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262