Ana Murnar Ranar Ƴancin Kai, An Buƙaci Shugaba Tinubu Ya Kori Wani Minista

Ana Murnar Ranar Ƴancin Kai, An Buƙaci Shugaba Tinubu Ya Kori Wani Minista

  • Jigon PDP, Dare Glintstone Akinniyi ya buƙaci Bola Ahmed Tinubu ya kori ministan Abuja, Nyesom Wike saboda ya cika surutu
  • Akinniyi ya yaba da ƙoƙarin wasu ministoci uku, inda ya ce sama da kaso 80% na muƙarraban shugaban ƙasa sun cancanci a sallame su
  • A wata hira da Legit.ng ranar Litinin, jagoran PDP ya ba shugaban ƙasa shawarar yadda ya kamata ya yi gyara a majalisar zartaswa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Mai magana da yawun ƙungiyar matasan PDP ta kasa, Dare Glintstone Akinniyi ya roƙi shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya tsige ministan Abuja, Nyesom Wike.

Akinniyi ya ba da shawarar a sallami Wike ne yayin da yake tsokaci kan shirin shugaba Tinubu na yin garambawul a majalisar zartaswansa.

Kara karanta wannan

Ranar ƴanci: Shugaba Tinubu ya yi magana kan farashin kayan abinci, ya faɗi mafita

Bola Tinubu da Wike.
Jigon PDP ya bukaci shugaban ƙasa ya sallami ministan Abuja, Nyesom Wike Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Nyesom Ezenwo Wike
Asali: Facebook

Wane dalili zai sa Tinubu ya kori Ministan Abuja?

A wata hira da Legit.ng ranar Litinin, 30 ga watan Satumba, 2024, Mista Akinniyi ya ce Wike ya jingine aikinsa na ministan Abuja, ya maida hankali kan siyasa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kuma bayyana cewa surutun Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas ya fi aikinsa yawa, yana jawowa gwamnati mai ci abin magana.

Akinniyi ya roƙi Tinubu kada ya kuskure ya kori ministoci uku, ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ministan ayyuka, Dave Umahi da ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo.

A cewarsa, in ban da waɗannan mutanen uku da ya ambata a sama, ya kamata shugaban ƙasa ya sallami dukkan sauran ministocin ya yi sabon zubi.

Akinniyi ya jero ministoci 3 da suka yi ƙoƙari

Jigon PDP ya ce:

"Da farko dai ina ba da shawarar a kori ministan Abuja, ya kawo hayaniya da surutu a wannan gwamnatin, riƙe mutum kamar Nyesom Wike bai dace ba."

Kara karanta wannan

Gwamna Abba ya gano matsalolin da suka hana Najeriya samun ci gaba

"Ministoci uku da suka haɗa da na harkokin cikin gida, ayyuka da sufurin jiragen sama sun yi zarra, amma ba ya ga su, duk a kori sauran."

Ranar ƴanci: Tinubu ya ɗauki alƙawari

A wani rahoton kuma Bola Ahmed Tinubu ya ƙara tabbatarwa ƴan Najeriya duk wahalar da suke kuka a kai za ta wuce kuma daɗi na nan tafe.

Shugabar ƙasar ya bayyana ƙoƙarin da gwamnatinsa ke yi domin abinci ya wadata da kuma rage farashinsa a faɗin ƙasar nan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262