Ana Raɗe Raɗin Gwamna na Shirin Sauya Sheƙa, Ciyamomi Sun Fice daga Jam'iyyar PDP

Ana Raɗe Raɗin Gwamna na Shirin Sauya Sheƙa, Ciyamomi Sun Fice daga Jam'iyyar PDP

  • Rahotanni sun nuna kantomomin da Gwamna Siminalayi Fubara ya nada sun fara barin jam'iyyar PDP zuwa APC a jihar Ribas
  • Hakan na zuwa ne bayan jita-jita ta fara yawo cewa shi kansa gwamna yana shirye-shiryen sauya sheƙa saboda rikicinsa da Nyesom Wike
  • Sai dai a lokacin da ya karɓi baƙuncin ƴan majalisar amintattun PDP kwanakin baya a Fatakwal, Fubara ya ce yana nan daram a jam'iyyar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rivers - Wasu daga cikin shugabannin ƙananan hukumomi na riƙon ƙwarya waɗanda Gwamna Siminalayi Fubara ya naɗa a jihar Ribas sun fice daga PDP.

Rahotanni sun nuna kantomomin sun sauya sheka daga PDP zuwa jam'iyyar APP a lokacin da ake shirye-shiryen zaben kananan hukumomi ranar 5 ga watan Oktoba, 2024.

Kara karanta wannan

Gwamna ya bi sahun Adamawa, ya faɗi watan da zai fara biyan sabon albashin N70,000

Gwamna Siminalayi Fubara.
Shugabannin ƙananan hukumomi na riko da Fubara ya nada sun fara barin PDP a Rivers Hoto: Sir Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

Punch ta tattaro cewa an fara yaɗa jita-jitar cewa Gwamna Fubara na shirin jefar da PDP, ya koma jam'iyyar APP saboda rikicinsa da ministan Abuja, Nyesom Wike.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Idan baku manta ba alaƙar Fubara da magabacinsa kuma tsohon ubangidansa Wike ta yi tsami wanda ya haifar da rikicin siyasa a jihar Ribas.

Gwamna Fubara ya musanta shirin barin PDP

Duba da yadda alamu suka nuna Wike ya karɓe ragamar PDP reshen jihar Ribas, ana fara raɗe-raɗin Gwamna Fubara na shirin sauya sheka zuwa APP.

Sai dai a lokacin da ya karɓi bakuncin ƴan majalisar amintattun PDP a Fatakwal, Gwamna Fubara ya musanta duk wata jita-jitar sauya sheƙa.

Amma a halin yanzu, wasu kantomimi na tsagin gwamnan tare da magoya bayansu sun fara fita daga PDP suna haɗewa da jam'iyyar APP, rahoton The Cable.

Kara karanta wannan

Tinubu ya shiga taron FEC ana rade raɗin za a kori wasu ministoci, bayanai sun fito

Ƴan tsagin Fubara sun tsaya takara a APP

Kusan dukkan ƴan takarar ciyamomi da kansiloli na tsagin Gwamna Fubara sun fara shirye-shirye ne a ƙarƙashin inuwar APP duk da cewa an fara yaƙin neman zaɓe.

Tuni dai fastocin kantoman ƙaramar hukumar birnin Fatakwal, Ezebunwo Ichemati da tambarin kamfen APP suka fara yawo a kwaryar birnin.

Da yake jawabi kwanan nan, Ichemati ya yi alkawarin samar da sahihin jagoranci ga al'umma idan aka zabe shi a matsayin shugaban ƙaramar hukumar birni.

Ƴan majalisar 27 sun yi nasara a kotu

A wani rahoton kuma kotu ta kori ƙarar da aka nemi maye gurbin ƴan majalisar dokoki 27 da ke goyon bayan Nyesom Wike a rikicin jihar Ribas.

Jam'iyyar APP ta kai ƙarar ƴan majalisar dokokin bisa sauya shekar da suka yi daga PDP zuwa APC, inda ta nemi a maye gurbinsu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262