Sakamakon Zaben Edo: Gwamna Ya Sha Kaye a Karamar Hukumarsa, APC Ta Yi Nasara

Sakamakon Zaben Edo: Gwamna Ya Sha Kaye a Karamar Hukumarsa, APC Ta Yi Nasara

  • Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ayyana jam'iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zabe a karamar hukumar Oredo, jihar Edo
  • INEC ta bayyana cewa APC ta samu kuri'u 30,780 a karamar hukumar Oredo a zaben gwamnan jihar Edo da aka gudanar a ranar Asabar
  • Karamar hukumar Oredo dai nan ce Gwamna Godwin Obaseki ya fito, inda kuma ya gaza ba jam'iyyarsa ta PDP nasara a cikinta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Edo - An bayyana jam’iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zaben gwamna a karamar hukumar Oredo ta jihar Edo, inda Gwamna Godwin Obaseki ya fito.

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana, Sanata Monday Okpebolo, dan takarar APC ya samu kuri’u 30,780 a karamar hukumar.

Kara karanta wannan

Zaben Edo: Ana jiran karamar hukuma 1, APC ta ba PDP tazarar kuri'u sama da 50,000

Gwamnan Edo, Godwin APC ya gaza kawowa PDP karamar hukumarsa ta Oredo
Edo: APC ta samu nasara a karamar hukumar Gwamna Obaseki. Hoto: @GovernorObaseki
Asali: Twitter

A yayin da APC ta yi nasara a karamar hukumar, jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa dan takarar PDP, Asue Ighodalo ya samu kuri’u 24,938.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Edo: Sakamakon zaben Oredo

Olumide Akpata na jam'iyyar Labour ya samu kuri'u 5,389.

A ƙasa akwai sakamakon da aka sanar a cibiyar tattara sakamako ta jihar da ke Benin.

Wadanda suka yi rijista -356242

Wadanda aka tantance -64802

Kuri'un da aka kada – 64042

APC – 30780

LP – 5389

PDP – 24938

APGA - 523

Duba wasu labarai a kan zaben Edo:

Edo 2024: Jami'an EFCC sun cafke masu sayen kuri'a ana tsaka da zabe

Sakamakon zaben Edo: APC ta lashe kananan hukumomi 10, PDP kuma 6

Zaben jihar Edo: Dan takarar PDP ya samu nasara a karamar hukumarsa

Akwai dalili: INEC ta yi barazanar soke zaben jihar Edo da aka dora a IReV

Kara karanta wannan

Tsohon kwamishina a Kaduna ya zama shugaban PDP, ya shirya ɗaiɗaita APC

"Dalilin ziyartar ofishin INEC" - Obaseki

A wani labarin, mun ruwaito Gwamna Godwin Obaseki ya ce ya ziyarci cibiyar tattara sakamako ta INEC da ke a jihar ne domin ya samu bayanai game da yadda abubuwa ke tafiya.

Hakazalika gwamnan ya ce ya je ofishin hukumar zaben ne domin ganawa da baturen zaben jihar don jin dalilin hana wakilan PDP shiga cibiyar tattara sakamakon zaben jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.