Sakamakon Zaben Edo: Dan Takarar APC Ya Lallasa Na PDP a Karamar Hukumar Oshiomole

Sakamakon Zaben Edo: Dan Takarar APC Ya Lallasa Na PDP a Karamar Hukumar Oshiomole

  • Jam'iyyar APC ta samu nasarar lashe zaɓen gwamnan jihar Edo a ƙaramar hukumar da Adams Oshiomole da Philip Shaibu suka fito
  • Ɗan takarar APC a zaɓen Monday Okpebholo ya samu ƙuri'u 32,107 inda ya lallasa takwaransa na PDP, Asue Ighodalo wanda ya samu ƙuri'u 17,483
  • Adams Oshiomole da Philip Shaibu sun taka rawar gani wajen ganin cewa ɗan takarar na APC ya samu nasara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Edo - Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Edo, Monday Okpebolo, ya samu nasara a ƙaramar hukumar Etsako ta Yamma.

Ƙaramar hukumar Etsako ta Yamma nan ne tsohon gwamnan jihar, Adam Oshiomhole da mataimakin gwamna Philip Shaibu suka fito.

Sakamakon zaben gwamnan Edo
Oshiomole ya lallasa PDP a karamar hukumarsa Hoto: @OfficialAPCNg
Asali: Twitter

APC ta yi nasara a ƙaramar hukumar Oshiomole

Kara karanta wannan

Zaben Edo: Dan takarar PDP ya fara karaya, ya zargi hukumar INEC

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Monday Okpebolo ya lallasa takwaransa na jam'iyyar PDP, Asue Ighodalo a ƙaramar hukumar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ɗan takarar na APC ya samu ƙuri’u 32,107 yayin da takwaransa na PDP, Asue Ighodalo, ya samu ƙuri’u 17,483.

Philip Shaibu ya koma jam’iyyar APC ne gabanin zaɓen bayan ya daɗe yana gwabzawa tsakaninsa da Gwamna Godwin Obaseki, wanda ya zaɓi Ighodalo a matsayin wanda yake son ya gaje shi.

Adams Oshiomole da Philip Shaibu na goyon bayan Monday Okpebholo domin ya zama gwamnan jihar Edo.

Karanta wasu labaran kan zaɓen Edo

Kara karanta wannan

Zaben Edo: 'Yan sanda sun dauki mataki bayan gwamna ya dira a ofishin INEC

APC ta lashe zaɓe a Esan

A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC ) na ci gaba da tattara sakamakon zaben gwamnan jihar Edo a babban ofishinta da ke birnin Benin.

Hukumar INEC ta bayyana jam'iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zabe a karamar hukumar Esan ta Yamma da tazarar kuri'u 1,948.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng