Sakamakon Zaben Edo: Dan Takarar PDP, Igholado Ya Samu Nasara a Karamar Hukumarsa
1 - tsawon mintuna
Edo - Dan takarar gwamnan jihar Edo a karkashin jam’iyyar PDP Asue Ighodalo ya yi nasara a karamar hukumarsa ta Esan ta Kudu maso Gabas.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
PDP ta samu kuri'u 14,199 inda ta doke jam'iyyar All Progressives Congress (APC) da ta samu 8,398, yayin da Labour Party ta samu kuri'u 98.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa har yanzu hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na ci gaba da tattara sakamakon zaben gwamna jihar na Edo.
Asali: Legit.ng