Edo: Ana Shirin Fadin Sakamakon Zaben Gwamna, 'Yan Sanda Sun Kara Matakan Tsaro

Edo: Ana Shirin Fadin Sakamakon Zaben Gwamna, 'Yan Sanda Sun Kara Matakan Tsaro

  • Magoya bayan jam'iyyu a Edo, yan siyasa da jama'ar gari na dakon a fadi sakamakon zaben gwamnan jihar
  • Tuni shirye-shirye su ka yi nisa, wanda ya sa rundunar yan sandan kasar nan ta tsaurara tsaro a Benin da kewaye
  • An kara yawan yan sanda da sauran matakan da za su tabbatar da an bi doka yayin da INEC ke sanar da sakamakon

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Edo - Yayin da aka kammala zaben gwamna a kananan hukumomi 18 na Edo, an fara shirin bayyana sakamakon zaben. Mutane sama da miliyan 2.2 suka cancanci fito wa kada kuri'arsu, amma kasa da 40% ne su ka yi zaben na ranar Asabar.

Kara karanta wannan

Zaben Edo: PDP, APC na zaman dari dari bayan INEC ta gaza fara tattara sakamako

Police
An kara yawan jami'an tsaro gabanin fadin sakamakon zaben Edo Hoto: Adejobi Olumuyiwa
Asali: UGC

BBC Hausa ta wallafa cewa an kara jibge jami'an yan sanda a babban birnin jihar, Benin gabanin bayyana sakamakon zaben.

Zabe: An kara jami'an tsaro a Edo

Rundunar yan sandan kasar nan ta kara yawan jami'an tsaro a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa da ke birnin Benin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matakin ya biyo bayan shirye-shiryen da ake yi na fadin sakamakon zaben gwamnan jihar da aka yi a ranar Asabar, kamar yadda jaridar Vanguard ta wallafa.

An jibge karnuka a ofishin INEC a Edo

Daga cikin matakan tsaro da rundunar yan sanda ta dauka akwai karin karnuka masu horo a birnin Edo da kewaye. An dauki matakin ne domin taimaka wa jami'an tsaro wajen tabbatar da tsaro yayin da ake tattara sakamakon zaben gwamna daga mazabu a babban ofishin INEC da ke Benin.

Kara karanta wannan

Akwai dalili: INEC ta yi barazanar soke sakamakon zaben Edo da aka dora a IReV

Gwamnan Edo ya fadi dalilin zuwa ofishin INEC

A baya mun ruwaito cewa gwamnan Edo, Godwin Obaseki ya fuskanci fushin yan sanda bayan ya ziyarci ofishin hukumar zabe ta kasa (INEC) yayin da zaben gwamna ke gudana a jihar.

Lamarin ya sa yan jam'iyyar adawa na APC tsunduma zanga-zanga bisa zargin za a iya yi masu rashin adalci, amma gwamnan ya ce gaza samun INEC a waya ne ya tilasta masa kai ziyarar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.