Edo 2024: PDP Ta Fara Korafi, Dan Takara Ya Fadi Makircin da APC Ta Shirya

Edo 2024: PDP Ta Fara Korafi, Dan Takara Ya Fadi Makircin da APC Ta Shirya

  • Yayin da ake cigaba da zaben jihar Edo, dan takarar jam'iyyar PDP ya yi korafi kan yadda lamura ke tafiya a yankinsa
  • Asue Ighodalo ya zargi jami'an tsro da cafke magoya bayan PDP ba tare da sun yi wani laifi na saba doka ba a zaben
  • Ighodalo ya kuma nuna damuwa kan yadda hukumar INEC ta yi jinkiri wurin kawo kayan aikin zabe a inda ya fi karfi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Edo - Dan takarar jam'iyyar PDP a zaben jihar Edo, Asue Ighodalo ya yi korafi kan abubuwan da ke faruwa.

Ighodalo ya nuna damuwa kan yadda jami'an tsaro ke kama magoya bayan jam'iyyar PDP a jihar.

Kara karanta wannan

Edo 2024: Ɗan takarar PDP ya koka, ya hango wata matsala ana tsaka da zaɓe

Dan takarar PDP a zaben Edo ya yi korafi kan neman kassara shi
Dan takarar PDP a zaben Edo, Asue Ighodalo ya zargi cafke yan jam'iyyar. Hoto: Asue Ighodalo
Asali: Facebook

Edo" Dan takarar PDP ya zargi jami'an tsaro

Premium Times ta ruwaito Ighodalo na fadin haka a mazabarsa da ke Ewohimi da ke karamar hukumar Esan ta Kudu maso Gabas.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dan takarar ya bayyana haka ne bayan kada kuri'a da misalin karge 10:40 na safe a yau Asabar 21 ga watan Satumbar 2024.

Ighodalo ya wasu daga cikin magoya bayan PDP da aka cafke babu abin da suka aikata saboda suna bakin layin zabe ne, cewar Punch.

Dan takarar PDP ya zargi shirin nakasa shi

Ya kuma bayyana samun wani rahoto cewa an samu jinkiri wurin fara gudanar da zabe a wuraren da yafi karfi a jihar.

"An tsayar da zabe har na fiye da awanni biyu a wuraren da na ke da karfi sosai."

- Asue Ighodalo

Ighodalo ya bukaci hukumar zabe ta INEC da ta kara wa'adin zaben a yankin Ewohimi bayan zabga ruwan sama da ya kawo cikas a zaben.

Kara karanta wannan

Zaben gwamnan Edo: Dan takarar jam'iyyar APC, Okpebholo ya kada kuri'arsa

INEC ta magantu kan rashawa a Edo

Kun ji cewa yayin da aka fara kada kuri'a a zaben jihar Edo, kwamishinar zabe ta bayyana shirin hukumar domin yin adalci.

Farfesa Rhoda Gumus ta ce ko nawa aka kawo mata na cin hanci ba za ta taɓa karba ba domin kare mutuncinta.

Farfesa Gumus ta ce ko kusa babu wanda ke da karfin halin da zai tunkare ta game da cin hanci ko biliyan nawa ne.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.