Ana Rade Radin Tuge Shi, Ganduje Ya Damƙi Sanata daga PDP Zuwa APC

Ana Rade Radin Tuge Shi, Ganduje Ya Damƙi Sanata daga PDP Zuwa APC

  • Jam'iyyar APC ta sake yin babban kamu bayan tsohon sanata ya sauya sheka daga PDP a jihar Edo ana shirin yin zaɓe
  • Sanata Francis Alimikhena wanda ya wakilci Edo ta Arewa ya watsar da PDP ne a yau Asabar 14 ga watan Satumbar 2024
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zaben jihar a ranar Asabar 21 ga watan Satumbar 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Edo - Yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zaben jihar Edo, jam'iyyar PDP ta yi babban rashi.

Tsohon sanatan Edo ta Arewa, Francis Alimikhena ya fice daga jam'iyyar mai mulkin jihar zuwa APC.

Kara karanta wannan

"Abin da ya faru a zabukan 2015, 2019 da 2023" Inji shugaban jam’iyyar PDP

Tsohon sanatan PDP ya koma APC ana shirin zabe
Tsohon Sanata, Francis Alimikhena, ya watsar da PDP tare da komawa APC. Hoto: Francis Alimikhena, official PDP.
Asali: Facebook

Edo: Tsohon Sanatan PDP ya dawo APC

Jigon APC a karamar hukumar Etsako ta Yamma, Zibiri Muhammed shi ya tabbatar da haka ga jaridar Punch.

Muhammad ya ce tsohon sanatan yanzu haka yana shirin dawowa da jiga-jigan PDP zuwa jam'iyya mai mulkin Najeriya.

Shugaban jam'iyyar APC ta kasa, Dakta Abdullahi Ganduje shi zai karbi sanatan a ranar kamfen karshe a jihar.

"Tabbas Sanata Alimikhena ya zama ɗan APC, ya koma jam'iyyar a hukumance a yau Asabar."
"Shugaban APC a Najeriya, Abdullahi Ganduje shi zai karbi sanatan a ranar karshe na kamfen zaben gwamnan jihar."

- Zibiri Muhammed

Yadda sanata ya gwabza da Adams Oshiomhole

Sanata Alimikhena ya wakilci Edo ta Arewa har sau biyu a Majalisar Dattawa ƙarƙashin APC, Daily Post ta ruwaito.

Kara karanta wannan

An zargi gwamna a Arewa da fatali da umarnin Tinubu, APC ta fusata da halayensa

Sanatan ya watsar da APC zuwa PDP bayan rasa tikiti ga Sanata Adams Oshiomhole a zaben 2023.

Bayan komawarsa PDP, sanatan ya tsaya takara, ya gwabza a zabe da Oshiomhole inda ya yi rashin nasara.

PDP ta ki sanya hannu a yarjejeniya

Kun ji cewa Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya yi fatali da bukatar tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar kan zabe.

Abdulsalami ya bukaci gwamnan ya sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya yayin zaben gwamnan da za a yi a Edo.

Sai dai gwamnan ya ce ba zai sanya hannu a yarjejeniyar ba saboda babu alamun zaman lafiya bayan cafke 'yan PDP 60.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.