Malami Ya Bayyana Hanya 1 da Za a Iya Kayar da Shugaba Tinubu a Zaɓen 2027

Malami Ya Bayyana Hanya 1 da Za a Iya Kayar da Shugaba Tinubu a Zaɓen 2027

  • Primate Elijah Ayodele ya bayyana dabarun da ya kamata ƴan adawa su yi idan suna son kayar da jam'iyya mai mulki a babban zaɓe na gaba
  • Fitaccen limamin cocin ya faɗi dabarun ne a lokacin da ƴan siyasa suka fara shirye-shiryen zaɓen 2027 a Najeriya
  • Ayodele ya ce shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu zai yi duk mai yiwuwa domin ya ci gaba da mulkin ƙasar nan har tsawon shekaru takwas

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Babban limamin cocin evangelical, Primate Elijah Ayodele ya ce tilas ƴan adawa su haɗa maja idan suna son kayar da shugaban kasa, Bola Tinubu a 2027.

Primate Ayodele ya buƙaci ƴan adawa su ajiye banbanci, su haɗe kai wuri ɗaya sannan su tsayar da ɗan takara ɗaya tilo da zai gwabza a zaɓen shugaban ƙasa na gaba.

Kara karanta wannan

"Arewa ta yi haƙuri," Sanatan Kaduna ya faɗi wanda ya kamata mutane su zaɓa a 2027

Primate Ayodele.
Primate Ayodele ya ce dole sai ƴan adawa su yiwa Bola Tinubu taron dangi a 2027 Hoto: Primate Babatunde Elijah Ayodele
Asali: Facebook

Malamin addinin kirista ya yi wannan furucin ne a wani faifan bidiyo da ya wallafa kwanan nan a shafinsa na manhajar X watau Twitter.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ayodele ya yi hasashen takarar Atiku

Idan baku manta ba Ayodele ya gargaɗi jam'iyyar PDP da kar ta sake ta yi kuskuren baiwa tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar takara.

Limamin cocin ya ce idan PDP ta sake ba Atiku takara a 2027, to ta zama gawa domin ba za ta kai labari ba.

Malamin ya faɗi hanyar kifar da Tinubi

A wannan karon kuma fitaccen limamin ya ce dole sai ƴan adawa sun dunƙule wuri ɗaya sannan za su iya turmushe Shugaba Tinubu a akwatun zaɓe.

"Idan kuna son kayar da Tinubu dole sai kun haɗa kai. Haɗuwar ku wuri ɗaya ne kaɗai zai iya kawo ƙarshen mulkin APC a zaɓen 2027.

Kara karanta wannan

Atiku ya fadi babban abin da ya dame shi bayan jigon PDP ya caccake shi

"Ku sani Bola Tinubi ba zai ɗauki lamarin da wasa ba, shi kansa ya shirya yaƙin, dole ku zauna ku lalubo dabaru masu ƙarfi don tunkarar 2027."

- Primate Ayodele.

Gwamnan Nasarawa ya gana da Ganduje

Kuna da labarin Gwamnan jihar Nasarawa ya ziyarci shugaban APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje a hekdkwar jam'iyyar da ke Abuja.

Abdullahi Sule ya gargaɗi ƴaƴan APC su kyale Ganduje ya fuskanci abubuwan da ke gabansa, ka da su ɗauke masa hankali.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262