Gwamnatin Tinubu Ta yi Martani bayan an Fara Maganar Haɗarin Zaben APC a 2027

Gwamnatin Tinubu Ta yi Martani bayan an Fara Maganar Haɗarin Zaben APC a 2027

  • Gwamnatin tarayya ta yi martani ga tsohon shugaba a jam'iyyar APC kan kalaman da ya yi a kan kamun ludayin shugaba Bola Tinubu
  • Jami'in shugaba Tinubu, Bayo Onanuga ne ya yi martanin inda ya ce a yanzu haka sun mayar da hankali a kan wasu abubuwa ne na musamman
  • Tsohon shugaba a jam'iyyar APC, Salihu Lukman ne ya caccaki gwamnatin Bola Tinubu kan zargin rashin tsari da manufa mai kyau

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta yi martani ga tsohon jigo a jam'iyyar APC, Salihu Lukman kan kalamai da ya yi a kan Bola Ahmed Tinubu.

Kara karanta wannan

Tinubu vs Buhari: Tsohon jigon APC ya 'fadi' shugaban da ya fi lalata kasa

Lukman Salihu ya ce ya kamata jam'iyyun adawa su hada kai wajen kayar da APC a zabe mai zuwa domin ceto Najeriya.

Shugaba Tinubu
Gwamnati ta yi martani ga Lukman Salihu. Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Source: Twitter

Jaridar Vanguard ta wallafa cewa jami'in shugaba Bola Tinubu a harkokin sadarwa, Bayo Onanuga ne ya yi martani a madadin gwamnatin tarayya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Maganar Salihu Lukman a kan Tinubu

Salihu Lukman ya ce an samu lalacewar harkokin gwamnati a karkashin mulkin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Haka zalika tsohon jigon APC ya ce Bola Tinubu ya gaza a kan Goodluck Jonathan yanzu kuma ya dauko hanyar gazawa kan abin da Muhammadu Buhari ya yi.

A karshe, Lukman ya bukaci jam'iyyun adawa da suke rikici da su nemi mafita domin kada Bola Tinubu ya samu zarcewa a 2027 saboda rashin hadin kansu.

Martanin gwamnati ga Lukman

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa a halin yanzu ba ta da lokacin da za ta rika musayar yawu da masu nuna adawa da tafiyar Tinubu.

Bayo Onanuga ya ce da sannu ayyukan da suke domin kawo canji a Najeriya za su ba dukkan yan kasa amsa kan irin maganganun.

Kara karanta wannan

Yusuf Bichi ya yi murabus: Tinubu ya nada sabon shugaban hukumar DSS

Daily Post ta ruwaito cewa Bayo Onanuga ya ce a yanzu haka sun mayar da hankali ne kan ciyar da Najeriya gaba wajen shugabanci nagari.

Lukman ya fadi kuskuren gwamnati

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon darakta-janar na kungiyar gwamnoni, Salihu Lukman ya yi martani kan illar da Bola Tinubu ke yiwa Najeriya.

Rahotanni sun nuna cewa Lukman ya ce tsare-tsaren tattalin arziki na Tinubu suna kashe tattalin kasar madadin farfado da shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng