Gwamna Abba Ya Naɗa Manjo Janar na Sojoji a Shirgegen Muƙamin Gwamnati a Kano

Gwamna Abba Ya Naɗa Manjo Janar na Sojoji a Shirgegen Muƙamin Gwamnati a Kano

  • Gwamna Abba Kabir ya naɗa Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris mai ritaya a matsayin sabon kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida
  • Abba Kabir ya sanar da wannan naɗin ne a wurin rantsar da majalisun gudanarwa da jami'o'i da manyan makarantu na jihar Kano
  • Ya buƙaci M.I Idris da ya yi amfani da gogewarsa ta sojoji wajen inganta sha'anin tsaro da zaman lafiya a faɗin jihar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya naɗa Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris (mai ritaya) a matsayin kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida.

Kimanin watanni biyar da suka gabata Gwamna Abba Kabir ya kirkiro ma'aikatar tsaro da harkokin cikin gida a Kano amma bai naɗa kwamishina ba a lokacin.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun sace kwamishina da matarsa a hanyar zuwa ɗaura auren ɗiyar gwamna

Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Gwamna Abba ya nada janar na sojoji a muƙamin kwamishina a Kano Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Gwamnan ya sanar da naɗin sabon kwamishinan ne a wurin bikin rantsar da majalisun gudanarwa na manyan makarantun Kano.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abba ya naɗa kwamishinan tsaro

Hakan na kunshe a wani faifan bidiyo da shafin Kwankwason Tuwita ya wallafa a manhajar X wanda aka fi sani da Twitter da yammacin ranar Jumu'a.

Ana sa ran naɗin tsohon babban jami'in sojan zai ƙara inganta tsaron cikin gida a Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

"Na amince da naɗin Manjo Janar M. I Idris (Mai ritaya) a matsayin kwamishina kuma mamban majalisar zartaswa ta jihar Kano.
"Bayan haka ina sanar da cewa zai jagoranci sabuwar ma'aikatar tsaron cikin gida," in ji Gwamna Abba.

Gwamnan Kano ya ja hankalin sabon kwamishinan

Gwamna ya buƙaci Manjo Janar Idris mai ritaya da ya tunkari ayyukan da ya rataya a wuyansa da kwazo da fasaha irin wanda ya nuna a lokacin aikinsa na soja.

Kara karanta wannan

Garambawul: Gwamna ya rantsar da kwamishinoni 6, ya kirkiro sababbin ma'aikatu

Abba Kabir ya kuma nanata muhimmancin sabuwar ma'aikatar na tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a faɗin jihar Kano.

Gwamna Abba ya gana kungiyar Qatar

A wani rahoton kuma gwamnatin jihar Kano karkashin Abba Kabir Yusuf ta gana da kungiyar kasar Qatar mai ba al'umma tallafi a fadin duniya.

Abba Kabir Yusuf ya kai ziyara ga kungiyar ne domin samar da hanyoyin yaki da talauci da inganta ilimi a Kano baki daya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262