Gwamnan PDP da Kansa Ya Yabawa Tsarin Tinubu, Ya Roki ’Yan Jiharsa a Arewa

Gwamnan PDP da Kansa Ya Yabawa Tsarin Tinubu, Ya Roki ’Yan Jiharsa a Arewa

  • Yayin da ake cigaba da zanga-zanga a Najeriya, Gwamna Ahmadu Fintiri ya roki al'ummar jihar Adamawa
  • Gwaman ya yi musu godiya kan gudanar da zanga-zanga ba tare da ta da tarzoma ba inda ya ce an ji kokensu
  • Fintiri ya tabbatar musu da cewa Bola Tinubu shugaba ne mai jin koken al'ummarsa kuma zai dauki mataki

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Adamawa - Gwamna Ahmadu Fintiri na jihar Adamawa ya roki al'ummar jihar kan zanga-zanga da ake yi.

Fintiri ya ce Shugaba Bola Tinubu mutum ne mai jin koken jama'a inda ya ce zai shawo kan matsalolin kasar.

Gwamna Fintiri ya roki al'umma kan tsare-tsaren Tinubu
Gwamnan Adamawa, Ahmadu Fintiri ya bayyana halin kirki na Bola Tinubu. Hoto: Ahmadu Fintiri.
Asali: Facebook

Zanga-zanga: Finitiri ya yabawa tsarin Bola Tinubu

Kara karanta wannan

Bidiyo: Jawabin Tinubu ya fara tasiri, matasa sun janye zanga zanga a birnin Legas

Gwamnan ya bayyana haka yayin jawabi ga 'yan jihar a yau Lahadi 4 ga watan Agustan 2024, cewar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Fintiri ya bukaci al'umma da su zauna lafiya da juna inda ya yaba musu kan yadda suka gudanar da zanga-zanga a jihar.

"Za mu yi aiki da ku domin tabbatar da an shawo ka bukatunku da kuke da su."
"Shugaba Bola Tinubu mutum ne mai jin koken jama'a kuma zai kawo karshen matsalolin kasar."

- Ahmadu Fintiri

Zanga-zanga: Fintiri ya yabawa al'ummar jihar Adamawa

Fintiri ya ce yana alfahari da 'yan jihar saboda yadda suka gudanar da zanga-zanga a kwanaki hudu cikin kwanciyar hankali.

Gwamnan ya kuma bukaci Shugaba Tinubu da ya yi mai yiwuwa wurin kawo karshen bukatun 'yan kasar.

Ya ce zamna lafiya ne kadai zai ba gwamnati damar gudanar da ayuukan cigaba a jihar.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Abubuwa 9 masu muhimmanci daga jawabin Shugaba Tinubu ga 'yan Najeriya

Tinubu ya magantu kan tallafin mai

Kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya yi magana kan dawo da tallafin man fetur da ya jefa al'umma cikin kunci a Najeriya.

Tinubu ya ce babu ranar dawo da tallafin saboda an cire shi ne saboda inganta tattalin arzikin kasar da ke cikin matsi.

Shugaban ya ce cire tallafin ya zama dole duk da ya san halin kunci da hakan ya jefa 'yan Najeriya a ciki na tsawon lokaci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.