An Ɗage Zanga Zangar da Matasa Za Su Fara Yau a Najeriya? Gaskiya Ta Bayyana

An Ɗage Zanga Zangar da Matasa Za Su Fara Yau a Najeriya? Gaskiya Ta Bayyana

  • A yau Alhamis, 1 ga watan Agusta, 2024 matasan Najeriya suka shirya fita zanga-zanga domin nuna fushinsu kan tsadar rayuwa
  • Sai dai wata sanarwa da ta bayyana da yammacin jiya Laraba, ta yi iƙirarin cewa masu shirya zanga-zangar sun ɗaga ta zuwa watan Oktoba
  • Fitaccen ɗan gwagwarmaya kuma ɗaya daga cikin waɗanda ake ganin su ne gaba a shirya zanga-zangar, Omoyele Sowore ya mayar da martani

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ikeja, jihar Lagos - Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwar jam'iyyar AAC, Omoyele Sowore ya musanta rahoton ɗaga zanga-zangar yunwa da za a fara yau Alhamis.

Sowore ya bayyana sanarwar da ke yawo cewa an sauya tsarin zanga-zangar a matsayin ƙarya mara tushe balle makama.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban ƙasa ta faɗi wasu manyan ƙusoshin gwamnati da hannu a zanga zanga

Omoyele Sawore.
Sawore ya musanta daga zanga zanga daga yau zuwa watan Oktoba, 2024 Hoto: @KolaSulaimon
Asali: Twitter

Ikirarin janye zanga-zanga daga Agusta

Legit Hausa ta fahimci cewa wata takarda ɗauke da sa hannun darektan shirye-shirye na ƙungiyar Take It Back Movement ta yi ikirarin cewa an canza ranar fara zanga-zanga.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce "saboda rashin tsaro da ake fama da shi," masu shirya zanga-zanga "sun yanke shawara mai tsauri" na dage ta zuwa ranar 1 ga Oktoba.

Gwamnatin tarayya ta sha nanata cewa tana gudun abin da zai je ya dawo shiyasa take ƙara rokon ƴan Najeriya sun janye shirinsu na zanga-zanga.

Da gaske an ɗage zanga-zanga?

Da yake mayar da martani a shafinsa na X, Sowore ya bayyana cewa hadiman Tinubu ko jami'an tsaro na Abuja ne ke yunkurin lalata shirin ƴan Najeriya.

Sowore, ɗaya daga cikin waɗanda ake ganin su ke shirya zanga-zangar ya ce babu fashi, za a fara wannan zanga-zanga gobe (yau) Alhamis.

Kara karanta wannan

Ana saura kwana 1, gwamnatin Tinubu ta aike da muhimmin saƙo kan zanga zanga

Haka nan kuma ƙungiyar Take It Back Movement ta musanta jita-jitar janye zanga-zanga.

Ƙungiyar ta wallafa a shafinta na X cewa:

"Ku yi watsi da sanarwar, sun fara yaɗa farfaganda da karerayin da suka saba."

Fadar shugaban ƙasa ta tona asiri

A wani rahoton na daban, fadar shugaban ƙasa ta zargi wasu masu karfin faɗa aji a gwamnati da hannu a shirya zanga-zangar da za a fara yau Alhamis.

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin ɗalibai, Sunday Asefon ne ya bayyana hakan a wani taro da aka shirya a Abuja.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262