Gwamnan PDP Ya Hango Matsaloli a Ƴancin Kananan Hukumomin Najeriya

Gwamnan PDP Ya Hango Matsaloli a Ƴancin Kananan Hukumomin Najeriya

  • Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya ce bai taɓa ɗaukar ko sisi daga kason kuɗin da ake turo ma kananan hukumomin jihar ba
  • Fasto Umo Eno ya yi maraba da hukuncin kotun koli na bai wa kananan hukumomi cikakken ƴancin karbar kason kudinsu daga tarayya
  • Ya ce matsalar da yake hangowa ita ce taya ciyamomi za su ɗauki nauyin biyan albashin ma'aikata a kan lokaci

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Akwa Ibom - Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya bayyana cewa hukuncin kotun ƙoli na bai wa kananan hukumomin damar cin gashin kansu zai taimaki gwamnatinsa.

Gwamna Eno na jam'iyyar PDP ya ce bai taba ɗaukar ko sisi daga cikin haƙƙin ƙananan hukumomi 23 na jihar ba tun da ya hau kan madafun iko.

Kara karanta wannan

Gwamna ya kafa kwamiti domin duba yiwuwar aiki da dokar kananan hukumomi

Fasto Umo Eno.
Gwamnan Akwa Ibom ya yi maraba da hukuncin bai wa kananan hukumomi ƴanci Hoto: Umo Eno
Asali: Facebook

Umo Eno ya bayyana haka ne yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai a filin jirgin sama na Uyo jim kaɗan bayan ya koma gida daga wata ziyarar aiki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda Vanguard ta ruwaito, gwamnan ya yi maraba da hukuncin kotun kolin wanda ya ce wani ƙarin raguwar nauyi ne ga gwamnatocin jihohi.

Gwamna Eno ya hango matsaloli

Sai dai gwamnan ya nuna damuwa kan yadda shugabanni a matakin ƙananan hukumomin za su aiwatar da tsarin cin gashin kai da kotu ta ba su, Daily Post ta kawo.

Fasto Eno ya nuna danuwa musamman kan yadda jagororin ƙananan hukumomin za su tafiyar da wasu abubuwa da za su koma kansu kamar biyan albashin ma'aikata a kan kari.

"Kotun koli ta yanke hukunci, ita ce kotu mafi ƙololuwa a ƙasar nan, amma mu a nan Akwa Ibom ba na tunanin muna da wata matsala, a wuri na wannan hukuncin ya yi daidai.

Kara karanta wannan

"Kotu ta yi adalci," Gwamnatin Abba ta jinjina hukuncin rikicin masarautun Kano

"Kalubalen da nake hange wanda ya kamata mu zauna mu nemo hanyar da za mu bi, shi ne taya za a rika biyan ma’aikatan kananan hukumomi albashi a kan lokaci?
“Ta ya za a biya malaman firamare albashi a kan kari? Ta yaya za mu biya bashin da ke kanmu? Ina fatan zamu lalubo hanyar da za a kaucewa kowace matsala."

- Gwamna Umo Eno.

Gwamna Fubara ya jaddada goyon bayan Tinubu

A wani rahoton kuma Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara na jam'iyyar PDP ya tabbatar da goyon bayansa ga shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.

Fubara ya kuma bukaci ƴan Najeriya su jingine duk wani banbanci da ke tsakani, su marawa gwamnatin tarayya baya don ta yi nasara.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262