Kotu Ta Tsige Ɗan Majalisar Tarayya, Ta Umarci Hukumar INEC Ta Shirya Sabon Zaɓe

Kotu Ta Tsige Ɗan Majalisar Tarayya, Ta Umarci Hukumar INEC Ta Shirya Sabon Zaɓe

  • Kotun sauraron ƙorafe-korafen zaɓe a jihar Sakkwato ta soke nasarar wani dan majalisar wakilan tarayya Umar Yusuf Sabo
  • Ta kuma umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta shirya sabon zaɓe a rumfunan zaɓe huɗu daga nan zuwa kwanaki 90
  • INEC za ta janye shaidar lashe zaɓen da ta bai wa Umar kana ta shirya zaɓe a rumfunan da hukuncin ya shafa a Yabo da Shagari

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto - Kotun sauraron ƙararrakin zaɓen ƴan majalisa ta tsige ɗan majalisar wakilan tarayya mai wakiltar Sabo da Shagari, Umar Yusuf Sabo.

Kotun ta kuma umarci Umar Sabo (Ɗanmaje) ya biya wanda ya shigar da ƙara N500,000 a matsayin ladan wahalar da shi.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya ji koken ƴan Najeriya, ya bada rallafin tirelolin shinkafa a jihohi 36

Umar Yusuf Yabo.
Kotun zabe ta tsige dan majalisar tarayya daga jihar Sakkwato Hoto: Umar Yusuf Yabo
Asali: UGC

Kotu ta soke zaben 'dan majalisa

Shugaban kwamitin alkalai uku na kotun mai shari'a Ashu A. Ewah ne ya karanto hukuncin, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana zaɓen da aka yi a mazaɓar Yabo/Shagari a matsayin wanda bai kammalu ba.

Sauran alkalan da suka yanke hukuncin sun haɗa da mai shari'a Helen N. Hamman Joda da mai shari'a Ali T. Changbo.

Dalilin soke nasarar Umar Yabo

Mai shari'a Ewah ya bayyana cewa zaɓen da INEC ta gudanar a 2023 da wanda ta ƙarasa a ranar 3 ga watan Fabrairu, 2024 cike yake da magudi.

Sakamakon haka ya umarci hukumar zaɓen ta sake shirya ƙarishen zaɓe cikin watanni uku masu zuwa domin tantance sahihin ɗan majalisar Yabo da Shagari.

Wuraren da za a sake zaben majalisa

Jaridar Leadership ta tattaro cewa za a gudanar da sabon zaɓen a rumfuna huɗu a ƙananan hukumomin Yabo da Shagari.

Kara karanta wannan

Bola Tinubu ya shiga taron FEC a Aso Rock, an yi shirun minti 1 saboda mutuwar Jigo

Runfunan zaɓen sun hada da Dagawa Maji Kira, Dagawa Mai Zane, Shiyar Magaji, Kesoji Shiyar Hakimi, Jaredi Maji Kira, da Mazoji.

Bugu da kari, kotun ta umarci INEC da ta karɓe takardar shaidar cin zabe da ta ba Umar Yusuf Yabo.

APC ta buƙaci matasa su ƙara hakuri

A wani rahoton kuma jam'iyyar APC mai mulki ta yi kira na musamman ga daukacin matasan Najeriya su dakatar da shirye-shiryen gudanar da zanga zanga.

Har ila yau, APC ta bayyana matakan da 'ya'yan jami'yyar ya kamata su dauka domin ganin ba a samu nasarar zanga zangar ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262