Gwamna Ya Dakatar da Babban Hadiminsa, Ya Umarci Ya Bar Ofis Nan Take

Gwamna Ya Dakatar da Babban Hadiminsa, Ya Umarci Ya Bar Ofis Nan Take

  • Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun ya dakatar da babban mataimakinsa na musamman kan harkokin jama'a, Emmanuel Adebisi ranar Laraba
  • Ya umarci dakatar da hadimin nan take har sai an yi bincike karkashin jagorancin shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin Osun, Kazeem Akinleye
  • Adeleke ya kuma umurci Kwamishinan Sufuri da ya tsara gudanar da taron sulhu a tsakanin bangarori masu adawa da juna

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Osogbo, jihar Osun - Gwamna Ademola Adeleke ya dakatar da Emmanuel Adebisi, babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin kungiyoyin fararen hula.

Mai magana da yawun gwamnan, Olawale Rasheed ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, 3, ga watan Yuli, 2024.

Kara karanta wannan

Borno: Majalisar dattawa ta faɗi sakacin da ya jawo aka kai harin bam a Gwoza

Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun.
Gwamna Ademola Adeleke ya dakatar da hadimi 1 a jihar Osun Hoto: @Osun_State_Gov
Asali: Twitter

Hadimi ya gamu da fushin gwamnan Osun

Gwamna Adeleke ya bayar da umarnin dakatar da hadimin nan take ba tare da ɓata lokaci lokaci ba, kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai gwamnan bai bayyana asalin dalilin da ya jawo ya ɗauki matakin dakatarwa kan Mista Emmanuel Adebisi ba.

A ruwayar Daily Post, sanarwar ta ce:

"Gwamna Adeleke ya dakatar da Emmanuel Adebisi nan take har sai an gama binciken da shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin jiha, Kazeem Akinleye zai jagoranta."

Gwamna Adeleke ya gargaɗi ma'aikatan sufuri

Bayan haka gwamnan ya gargaɗi ma'aikatan sufuri a faɗin jihar Osun da su gujewa duk wani abu da zai kawo tada zaune tsaye.

Ya umurci Kwamishinan Sufuri na jihar Osun da ya shirya wani taron sasantawa domin sulhunta dukkan bangarorin harkar sufuri da ke faɗa da juna..

Kara karanta wannan

Gidan tsohon gwamna, Okorocha ya ruguje, katafaren gini ya danne mutane a Abuja

"Jami'ai da sauran mambobin ƙungiyar sufuri su guji kauda hankalin al'ummar jihar Osun daga ayyukan aherin da ake yi, gwamnati ba za ta lamunci duk wani nau'in tayar da tazoma ba.
"Ba za mu bari a mayar da hannun agogo baya ba, gwamnati mai ci ba za ta raga wa kowa kan tada yamutsi ba. Duk wata matsala da ta taso a bangaren sufuri, ya kamata a shawo kanta cikin ruwan sanyi."

- Gwamna Ade,ola Adeleke.

Gwamna Alia ya sa dokar kulle

Kuna da labarin Gwamna Hyacinth Alia ya sanya dokar zaman gida a karamar hukumar Ukum da kewayenta biyo bayan zanga-zangar da ta ɓarke ranar Laraba.

Matasa sun ɓarke da zanga-zanga a Sankera, hedkwatar da ƙaramar hukumar Ukum ne sakamakon kisan mutane 11 a yankin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel