Ana Daf da Zabe, PDP Ta Sallami Tsohon Mataimakin Gwamna da Jiga Jiganta 2

Ana Daf da Zabe, PDP Ta Sallami Tsohon Mataimakin Gwamna da Jiga Jiganta 2

  • Jam'iyyar PDP a jihar Edo ta kori tsohon mataimakin gwamnan jihar, Philip Shaibu kan zargin cin dunduniyarta
  • Jam'iyyar ta dauki wannan matakin ne bayan ganawar kwamitin gudanarwa na PDP ana daf da gudanar da zabe
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zaben gwamnan jihar a watan Satumbar 2024 mai kamawa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Edo - Ana daf da zaben gwamnan jihar Edo, jam'iyyar PDP ta kori tsohon mataiimakin gwamnan jihar, Philip Shaibu.

Jam'iyyar ta dauki matakin ne bayan zargin Shaibu da cin dunduniyarta ana saura watanni uku a yi zaben gwamnan jihar.

PDP ta sallami tsohon mataimakin gwamna a Edo kan cin amana
Jam'iyyar PDP a jihar Edo ta kori Philip Shaibu da jiga-jiganta 2. Hoto: Philip Shaibu.
Asali: Facebook

Edo: PDP ta sallami Philip Shaibu

Kara karanta wannan

PDP ta tsoma baki kan rikicin Ribas, yayin da APC ke neman a sanya dokar ta baci

Kwamitin gudanarwa na jam'iyyar ya kuma sallami mataimakin shugaban jam'iyyar ta kasa a yankin Kudu maso Kudu, Dan Orbih a cewar Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na kunshe a cikin wata sanarwa da kakakin jam'iyyar a jihar, Ogie Vasco ya fitar a yau Laraba 19 ga watan Yuni.

Vasco ya ce jam'iyyar ta dauki wannan matakin ne bayan tuntubar duka masu ruwa da tsaki inda ya ce korar za ta fara aiki ne nan take, TheCable ta tattaro.

An tsige Philip Shaibu daga mukaminsa

Wannan na zuwa ne bayan Majalisar jihar Edo ta tsige Shaibu a matsayin mataimakin gwamnan jihar a watan Afrilun 2024.

Tsigewar na zuwa ne bayan kafa kwamiti mai mambobi bakwai domin kaddamar da binciken kan zarge-zarge da ake yi masa.

Daga cikin zarge-zargen akwai ba da shaidar karya da bankada bayanan sirri na gwamnatin jihar ba bisa ka'ida ba.

Kara karanta wannan

An shirin zaben gwamna, jigon PDP ya yi maƙarƙashiya, jam'iyya ta kore shi

PDP ta sallami tsohon 'dan Majalisar Tarayya

A wani labarin, kun ji cewa jam'iyyar PDP a jihar Edo ta sallami tsohon mamban Majalisar Tarayya, Omorgie Ihama kan wasu zarge-zarge.

Jam'iyyar ta dauki wannan matakin ne ana daf da gudanar da zaben gwamnan jihar a watan Satumbar 2024 wanda zamu shiga.

Kakakin jam'iyyar a jihar, Ogie Vasco shi ya tabbatar da haka inda ya ce ana zargin Ihama da cin dunduniyarta.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel