Tsohon Shugaban Ƙasa Ya Faɗi Wasu Gwamnoni da Ke Amfani da Ƴan Daba Su Murde Zaɓe

Tsohon Shugaban Ƙasa Ya Faɗi Wasu Gwamnoni da Ke Amfani da Ƴan Daba Su Murde Zaɓe

  • Dakta Goodluck Ebele Jonathan ya zargi wasu gwamnonin jihohi da amfani da ƴan daba wajen maguɗin zaɓe don cimma burinsu na siyasa
  • Tsohon shugaban ƙasar ya ce maimakon gwamnoni su gina matasan ta hanyar da gwamnati za ta amfana da su, sun zaɓi mayar da su ɓata gari
  • Jonathan ya yaba da yadda Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo ya ɗauki yaran da suka kammala digiri da daraja ta farko aiki

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Edo - Tsohon shugaban ƙasa, Dr. Goodluck Jonathan, ya yi zargin cewa wasu gwamnoni na amfani da ɓata gari wajen cimma burinsu na siyasa.

Jonathan ya ce gwamnonin sun mayar da hankali wajen shirya ɓata gari don maguɗin zaɓe, maimakon su taimaka masu su zama kwararru a aikin gwamnati.

Kara karanta wannan

"Ba faɗuwa na yi ba" Bola Tinubu ya yi magana kan abin da ya faru a Eagle Square

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan.
Jonathan ya soki gwamnonin da ke amfani da ƴan daba su murde zabe Hoto: Dr. Goodluck Jonathan
Asali: Getty Images

Ya bayyana haka ne a Benin ranar Laraba a wurin kaddamar da sakatariyar jihar Edo da Gwamna Godwin Obaseki ya sabunta, Daily Trust ta kawo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tsohon shugaban kasar ya ce lokacin da shugaban ma’aikatan Edo ya sanar cewa Obaseki ya dauki ɗaliban da suka gama digiri da shaida mafi daraja aiki, ya ji dadi matuka.

Jonathan ya soki wasu gwamnoni

"Mutum mai hangen nesa kamar Obaseki ne kaɗai zai iya haka. A taƙaice mun zo wani zamani da idan ka je wasu jihohin za ka ga gwamnoni suna shirya ɓata gari saboda siyasa.
"Suna ƙarafafawa ɓata gari guiwa domin su yi amfani da su wajen murde zaɓe, su sato akwatu, su ɗauki wukake da makamai su nufi mutane a wurin zaɓe.
"Amma a nan Edo kana ƙarfafa masu hazaƙa, mutane masu hazaka ba ƴan jam'iyya ɗaya ba ne, akwai su a kowace jam'iyya."

Kara karanta wannan

Gwamnatin tarayya ta fadi dalilin sake cin bashin Dala 2.5bn

- Goodluck Jonathan.

Tun da farko, Gwamna Obaseki ya ce ya gyara sakatariya saboda yana da yaƙinin cewa dole sai tsare-tsaren gwamnati sun tafi daidai za a samu ci gaba a jihar, Gazette Nigeria ta rahoto.

Tinubu ya faɗi dalilin zamewa a Abuja

A wani rahoton Bola Ahmed Tinubu ya yi magana a karon farko kan zamewar da ya yi ya faɗi a lokacin hawa motar fareti a birnin tarayya Abuja.

Shugaban ƙasar ya bayyana cewa shi ɗan yarbawa ne kuma ya ɗan taɓa wasan al'adar da ake kira dobale domin murnar ranar dimokuraɗiyya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel