Zaben Gwamna: APC Ta Rasa Babban Jigon da Take Ji da Shi, Ya Samu Matsayi a NNPP

Zaben Gwamna: APC Ta Rasa Babban Jigon da Take Ji da Shi, Ya Samu Matsayi a NNPP

  • Barista Olugbenga Edema ya zama ɗan takarar gwamnan jihar Ondo a inuwar NNPP bayan ya baro All Progressives Congress (APC)
  • Tsohon jigon jam'iyya mai mulki ya ce ya shirya sauke Gwamna Lucky Aiyedatiwa daga mulki a zaɓen watan Nuwamba, 2024
  • NNPP ta ba Edema tikitin takara ne bayan tsohon ɗan takararta, Oluwatosin ya janye daga takara bisa ra'ayin kansa da kishin jam'iyya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Ondo - Barista Olugbenga Edema, ɗaya daga cikin manyan ƴan takarar APC da suka nemi tikitin takarar gwamna a jihar Ondo ya koma New Nigeria People’s Party (NNPP).

Jim kaɗan bayan haka NNPP ta miƙawa Barista Edema tikitin takarar gwamna a zaɓen jihar Ondo da za a yi ranar 16 ga watan Nuwamba, 2024.

Kara karanta wannan

"Yadda Tiinubu yake biyan tallafin fetur bayan sanar da soke tsarin tun ranar farko"

Jam'iyyar NNPP.
Jam'iyyar NNPP ta sake tsayar da ɗan takarar gwamna a jihar Ondo Hoto: New Nigeria People’s Party (NNPP)
Asali: Twitter

NNPP tayi sabon 'dan takara a Ondo

Edema ya zama ɗan takarar NNPP ne a zaɓen fitar da gwani da jam'iyyar ta shirya a Akure, babban birnin jihar Ondo ranar Laraba, jaridar Leadership ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An shirya zaben ne domin maye gurbin tsohon ɗan takarar gwamna, Ayeni Oluwatosin, wanda ya janye niyyar takara haka kurum.

Barista Edema ya bugi ƙirjin cewa ya shirya kayar da da ɗan takarar APC kuma gwamna mai ci, Lucky Aiyedatiwa idan a akwatun zaɓe.

Meyasa ɗan takarar NNPP ya janye?

A wasiƙar da ya miƙa domin tabbatar da janyewa daga takara, Mista Oluwatosin ya ce ya ɗauki matakin ne domin ɗaga ƙimar NNPP.

“Ni, Ayeni, Oluwatosin Israel, dan takarar gwamna a NNPP a zaben da za a yi ranar 16 ga Nuwamba, 2024 a jihar Ondo, na haƙura da takara.

Kara karanta wannan

Fitaccen basarake kuma tsohon kwamishinan ƴan sanda ya kwanta dama

"Ba don komai na janye daga takara ba sai don ina kishin jam'iyyata NNPP," in ji shi.

NNPP za ta tsaida 'dan takarar gwamna

Haka nan kuma Mista Peter Olagookun, shugaban NNPP na jihar Ondo ya tabbatar da janyewar dan takarar, kamar rahoton Vanguard ya kawo.

Ya ce babu wanda ya tilasta masa, ya janye ne bisa ra'ayin kansa kuma domin ya ba NNPP damar zaƙulo ɗan takarar da zai baiwa maraɗa kunya.

Atiku ya ce tallafin mai ya dawo

A wani rahoton kuma, an ji Atiku Abubakar ya buƙaci shugaban ƙasa ya fito ya faɗawa ƴan Najeriya gaskiya game da biyan tallafin man fetur.

Wazirin Adamawa ya yi ikirarin cewa cire tallafi duk maganar baka ce, inda ya ce kuɗin tallafin bana watau shekarar 2024 ka iya kai wa N5.4trn.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel