Ana Daf da Zabe, Ɗan Takara a Jam'iyyar Kwankwaso Ya Janye Daga Neman Gwamna

Ana Daf da Zabe, Ɗan Takara a Jam'iyyar Kwankwaso Ya Janye Daga Neman Gwamna

  • Ɗan takarar jam'iyyar NNPP a zaben jihar Ondo, Israel Ayeni ya yanke shawarar janye takara daga zaben watan Nuwambar
  • Ayeni ya tabbatar da haka a yau Laraba 5 ga watan Yuni inda ya ce ya dauki matakin ne domin jam'iyyar NNPP
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zaben gwamna a jihar a ranar 16 ga watan Nuwamba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Ondo - Ɗan takarar gwamna a jam'iyyar NNPP a jihar Ondo ya janye daga kudirinsa na neman takara.

Mista Israel Ayeni ya tabbatar da janye takarar a yau Laraba 5 ga watan Yuni a birnin Akure da ke jihar.

Kara karanta wannan

Zaɓen 2024: APC ta rasa babban jigon da take ji da shi, ya samu matsayi a NNPP

Dan takarar jam'iyyar NNPP da Kwankwaso ya ke ya janye daga neman gwamna
Dan takarar jam'iyyar NNPP a Ondo, Israel Ayeni ya janye daga takara.
Asali: Original

NNPP: Ayeni ya lashe zaben fidda gwani

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ya bayyanawa ƴan jaridu inda ya ce ya yi haka ne saboda ci gaban jam'iyyar, cewar Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ɗan takarar ya yi nasarar lashe zaben fidda gwani da kuri'u 100 kan Farfesa Ibrahim Ajagunna da aka gudanar a ranar 26 ga watan Afrilu, TheCable ta tattaro.

"Ni Israel Ayeni, dan takarar jam'iyyar NNPP a zaben 16 ga watan Nuwamba a Ondo na janye takarar neman gwamna."
"Na yanke shawarar janye takarar ne domin kare muradun jami'iyyar NNPP."

- Israel Ayeni

APC ta dakatar da ƴar takarar gwamna

Har ila yau, jam'iyyar APC a gundumar Ode-Aye a karamar hukumar Okitipupa a jihar Ondo ta dakatar da Injiniya Folake Omogoroye.

Injiniya Folake Omogoroye ita ce ƴar takara mace da ta fafata a zaɓen fitar da gwani na jam'iyyar APC da aka gudanar ranar 20 ga watan Afrilun 2024.

Kara karanta wannan

PDP ta watsawa Atiku ƙasa a ido kan hadaka da Kwankwaso, Obi, ta yi alfahari

Kwankwaso ya magantu kan matsalolin Arewa

A wani labarin, kun ji cewa Sanata Rabiu Kwankwaso ya magantu kan tabarbarewar lamura da suka addabi yankin Arewacin Najeriya.

Kwankwaso ya bayyana rashin iya shugabanci da rashin adalci a matsayin manyan abubuwa da ke lalata lamura a yankin.

Tsohon gwamnan Kano ya koka kan yadda ake yaudarar mutane da atamfa da taliya domin zaben azzaluman shugabanci.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel