Ganduje: Wasu Ƴan Arewa Sun Kunno Wuta Kan Kujerar Shugaban APC Na Ƙasa

Ganduje: Wasu Ƴan Arewa Sun Kunno Wuta Kan Kujerar Shugaban APC Na Ƙasa

  • Shugaban APC na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje na ci gaba da fuskantar adawa daga yankin Arewa ta Tsakiya
  • Kungiyar ƴaƴan APC sun fara neman goyon baya domin kwato kujerar shugaban jam'iyyar APC daga hannun Ganduje
  • A cewar shugaban ƙungiyar, ba za wu yi ƙasa a guiwa ba wajen dawo da kujerar kuma tuni suka kai ƙara gaban kotu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Wata kungiyar mambobin jam'iyyar APC a Arewa da Tsakiya ta yi kira ga masu faɗa a ji na shiyyar su fito su mara mata baya wajen kwato kujerar shugaban jam'iyya mai mulki.

Ƙungiyar ta nemi fitattun ƙungiyoyi kamar lauyoyi da ƙungiyoyin fararen hula su haɗa kai domin sauke Dakta Abdullahi Ganduje daga kujerar shugaban APC na ƙasa.

Kara karanta wannan

Atiku Abubakar ya faɗi dalilin da zai sa ya goyi bayan Peter Obi a zaben 2027

Shugaban APC na ƙasa, Ganduje.
Kungiyar APC ta fara neman goyon baya domin sauke Ganduje Hoto: Dr. Abdullahi Umar Ganduje
Asali: Twitter

Shugaban ƙungiyar, Alhaji Saleh Mandung Zazzaga, ne ya yi wannan kira yayin zantawa da manema labarai a Jos, babban birnin jihar Filato ranar Jumu'a.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce kujerar da Ganduje ke zaune a kai ta shiyyar Arewa ta Tsakiya kamar yadda jam'iyyar APC ta tsara, cewar rahoton jaridar Leadership.

Alhaji Sale ya ce kamata ya yi wani ɗan jihar Nasarawa ko ɗan Arewa ta Tsakiya ya maye gurbin Abdullahi Adamu amma ba Ganduje ba wanda ya fito daga Arewa maso Yamma.

Ganduje na fuskantar matsala

Ya ƙara da cewa gundumar Ganduje a jihar Kano ta kaɗa masa ƙuri'ar rashin amincewa da dakatar da shi, sannan kuma an shigar da Ganduje ƙara a kotu.

Shugaban ƙungiyar ta APC ya ce saboda haka ne suka fito suka fara neman a dawo masu da kujerar shugaban jam'iyya wadda aka ƙwace da ƙarfi.

Kara karanta wannan

"Mu taimaka masu," Ganduje ya yi magana kan mummunan harin da aka kai Masallaci a Kano

A cewarsa, wannan dalilin ne ya sa suke neman fitattun ƙungiyoyi su haɗa kai da su domin cimma nasara a wannan kudiri da suka sanya a gaba.

Ya ce ba a APC kaɗai ba, duk inda suka ga za a mayar da Arewa ta Tsakiya saniyar ware, ko a yaudari yankin, sai inda ƙarfinsu ya ƙare, Daily Post ta tattaro.

Zazzaga, mamban kwamitin kamfen shugaban kasa a zaben da ya gabata ya ce za a ci gaba da sauraron karar da kungiyar ta shigar da Ganduje a ranar 30 ga watan Mayu.

Jerin ministocin Tinubu da suka fi ƙoƙari

A wani rahoton kuma Deji Adeyanju, mai fafutukar kare hakkin ɗan adam ya tantance ministocin da suka fi ƙoƙari da marasa amfani a Gwamnatin Bola Tinubu.

Adeyanju ya raba ministocin zuwa rukuni biyu, jerin masu koƙari da kuma rukunin ƴan zaman dumama kujera bisa la'akari da ayyukansu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel