Shugaba Tinubu Ya Nada Ali Nuhu Mukamin Shugaban Hukumar Fina-Finai ta Najeriya

Shugaba Tinubu Ya Nada Ali Nuhu Mukamin Shugaban Hukumar Fina-Finai ta Najeriya

  • Ma'aikatar Fasaha, Al'adu da Tattalin Arzikin Fikira ta tarayya ta kara inganta tare da sabbin daraktoci guda 11
  • An nada wadannan sabbin daraktoci ne bisa ga umurnin Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
  • Wata sanarwa daga fadar shugaban kasa ta tabbatar da nadin nasu a ranar Juma'a, 12 ga watan Janairu, kamar yadda Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

FCT, Abuja - Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin sabbin daraktoci 11 a ma'aikatar Fasaha, Al'adu da Tattalin Arzikin Fikira.

Wadannan daraktoci za su shugabanci hukumomi daban-daban a karkashin ma'aikatar, ciki harda majalisar kula da fasaha da al’adu ta kasa, hukumar tace fina-finai ta kasa, da kuma gidan tarihi na kasa.

Kara karanta wannan

Cikakkun sunaye: Abba Yusuf, Caleb Mutfwang da gwamnoni 8 da Kotun Koli ta tabbatyar da nasarorinsu

Tinubu ya nada sabbin daraktoci
Tinubu Ya Nada Ali Nuhu, Obi Asika da Wasu 9 a Matsayin Daraktoci a Ma’aikatar Al’adu Hoto: Fadar shugaban kasa
Asali: Facebook

Su wanene sabbin daraktocin da aka nada?

Kamar yadda yake kunshe a cikin wata sanarwa da kakakin shugaban kasar, Ajuri Ngelale, ya fitar, daraktocin sun hada da:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

(1) Tola Akerele — Darakta Janar, Cibiyar al'adu ta kasa

(2) Dr Shaibu Husseini — Darakta Janar na Hukumar Tace Fina-Finai ta Kasa

(3) Mista Obi Asika - Darakta Janar na Majalisar al'adu ta kasa

(4) Aisha Adamu Augie — Darakta Janar na Cibiyar al’adun bakar fata da Afirka

(5) Ekpolador-Ebi Koinyan — Shugaban gidan ajiye kayan yaki na tarihi

(7) Chaliya Shagaya — Darakta Janar, makarantar kayan tarihi na kasa

(8) Hajiya Khaltume Bulama Gana — Babban daraktan gidan rawa ta kasa

10) Ali Nuhu — Shugaban Cibiyar fina-finai na Najeriya

(11) Ramatu Abonbo Mohammed - Darakta Janar, Hukumar kula da gidajen tarihi da abubuwan tarihi ta kasa

Kara karanta wannan

Bayan dakatar da N-Power, Tinubu ya dauki matakin karshe kan shirin NSIPA, ya fadi dalili

Sanarwar ta bayyana cewa, shugaban kasar ya umurci wadanda aka nada da su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu tare da bin ka’idoji bisa kwarewa, kwazo da kishin kasa.

Manufar ita ce habbakawa da karfafa bangaren fikira.

Tinubu ya dakatar da shirin NSIPA

A gefe guda, mun ji a baya cewa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da dukkan shirye-shiryen da hukumar ba da tallafin dogaro da kai ta kasa (NSIPA) ke gudanarwa, rahoton Leadership.

Daraktan labarai a ofishin Sakataren gwamnatin tarayya, Segun Imohiosen, ne ya sanar da ci gaban a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a, 12 ga watan Janairu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng