Kotun Koli Ta Ayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Legas

Kotun Koli Ta Ayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Legas

  • Kotun Koli ta tabbatar da zaben Babajide Sanwo-Olu na jam'iyyar APC a matsayin gwamnan jihar Legas
  • Kwamitin mai mutum biyar a cikin hukuncinsa wanda masu shari’a Lawal Garba da Adamu Jauro suka yanke, sun tabbatar da ayyana sanwo-Olu a matsayin wanda ya lashe zaben
  • Kotu ta yi watsi da kararraki guda biyu da ke kalubalantar nasarar Gwamna Sanwo-Olu a zaben ranar 18 ga Maris, 2023

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Kotun Kolin Najeriya a ranar Juma'a, 12 ga watan Janairu, ta tabbatar da zaben Babajide Sanwo-Olu a matsayin zababben gwamnan jihar Legas.

Kamar yadda jaridar The Nation ta rahoto, Maishari'a Garba Lawal wanda ya karanto hukuncin ya yi watsi da karar da Gbadebo Rhodes-Vivour na jam'iyyar LP ya shigar.

Kara karanta wannan

Kotun koli ta ƙara yanke hukunci kan sahihancin nasarar gwamnan adawa, PDP ta yi warwas

Kotun Koli ta tabbatar da zaben Gwamna Babajide Sanwo-Olu
Yanzun Nan: Kotun Koli Ta Ayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Legas Hoto: Babajide Sanwo-Olu
Asali: Getty Images

A cewar Mai shari'a Lawal, Gwamna Sanwo-Olu da mataimakinsa, Obafemi Hamzat, sun cancanci tsayawa takarar zaben gwamnan jihar Legas na 2023.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotun Koli ta kori karar Rhodes-Vivour

A hukuncin da ta yanke, Kotun Kolin ta bayyana cewa karar da Rhodes-Vivour ya shigar bai dace ba.

A cewar kotun, samun takardar shaidar zama dan kasar Amurka (Amurka) damataimakin Sanwo-Olu, Hamzat ya yi, bai hana shi zama dan Najeriya ba, kasancewar shi haifaffen dan kasa.

Kotun ta tabbatar da hukuncin kotun daukaka kara da ta tabbatar da zaben Sanwo-Olu.

Kotun koli ta yi watsi da karar Adediran na PDP

Har ila yau, kotun ta yi watsi da karar da dan takarar jam’iyyar PDP, Azeez Adediran (Jandor) ya shigar, inda ya nemi ta tsige gwamna Sanwo-Olu, rahoton The Cable.

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar neman tsige gwamnan APC, bayanai sun fito

Kotun ta ce shari’ar Adediran ba ta da tushe.

Gwamnoni sun isa Kotun Koli

A baya mun kawo cewa yayin da Kotun Koli ke shirin yanke hukunci kan takaddamar zabukan wasu gwamnonin jihohi, a kalla gwamnoni hudu ne suka isa babbar kotun don zaman hukuncin.

Gwamnoni hudu da suka isa Kotun Kolin sune Bala Mohammed na jihar Bauchi, Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, Caleb Mutfwang na jihar Filato da kuma Dauda Lawal na jihar Zamfara, rahoton The Nation.

Simon Lalong, tsohon gwamnan jihar Filato ma ya hallara a Kotun Kolin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags: