Badakalar N585m: Tinubu Ya Naɗa Wanda Zai Maye Gurbin Ministar da Ya Dakatar, Ya Kama Aiki

Badakalar N585m: Tinubu Ya Naɗa Wanda Zai Maye Gurbin Ministar da Ya Dakatar, Ya Kama Aiki

  • Abel Olumuyiwa Enitan ya karɓi ragamar jagorancin ma'aikatar jin ƙai da yaƙi da talauci bayan dakatar da Betta Edu
  • Babban sakataren ma'aikatar ya maye gurbin Edu ne bisa umarnin shugaban ƙasa, Bola Tinubu, wanda ya dakatar da ministar ranar Litinin
  • Manyan masu faɗa a ji da shugabanni a ɓangarorin Najeriya sun yabawa Tinubu bisa wannan mataki da ya ɗauka kan Edu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Sakamakon dakatarwar da aka yi wa ministar harkokin jin ƙai da yaye Talauci, babban sakataren ma’aikatar, Abel Olumuyiwa Enitan, ya karɓi ragamar jagorancin ma’aikatar.

Matakin da ya ɗauka ya yi daidai da umarnin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, wanda ya dakatar da Betta Edu ranar Litinin, 8 ga watan Janairu, 2024.

Kara karanta wannan

Badaƙala: EFCC ta tatsi muhimman bayanai, ta ɗauki mataki kan ministar da Tinubu ya dakatar

Shugaba Tinubu da Betta Edu.
Badakalar N585m: Babba Sakatare Ya Maye Gurbin Betta Edu a Ma'aikatar Jin Kai Hoto: Ajuri Ngelale, Betta Edu
Asali: Twitter

Shugaban ƙasar ya dakatar da ita ne bisa zargin tura wasu kuɗaɗen ma'aikatar da take jagoranta zuwa asusun kai da kai, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mista Enitan ya haye kujerar shugabancin ma'aikatar jin ƙai

Bayanai sun nuna cewa babban sakataren ya karɓi ragamar jagorancin ma'aikatar jin ƙai ne bayan samun umarnin hakan a wata wasika daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya.

Dama tun da farko, Tinubu ta bakin mai magana da yawunsa, Ajuri Ngelale, ya umarci dakatacciyar ministar ta miƙa ragamar ma'aikatar jin ƙai ga babbban sakatare.

A rahoton The Nation, sanarwan ta ce:

“Shugaban ƙasa ya kuma umurce ta da ta baiwa hukumomin bincike cikakken hadin kan da suke buƙata yayin aikinsu na bincike kan badaƙalar."

Bugu da ƙari, shugaba Tinubu ya umarci wani kwamiti karkashin ministan tattalin arziki da ministan kuɗi su bincike ayyuka da tsare-tsaren da ke ƙarƙashin ma'aikatar.

Kara karanta wannan

Betta Edu: EFCC ta titsiye shugabannin bankuna 3 kan badakalar N44bn, bayanai sun fito

Wannan mataki da Bola Tinubu ya ɗauka na shan yabo daga kowane ɓangare na ƙasar nan. Wasu na ganin cewa tauna tsakuwa ne domin aya ta shiga taitayinta.

Gwamna Bello ya rushe majalisar zartarwa

A wani rahoton Gwamna mai barin gado, Yahaya Bello, ya sallami dukkan mambobin majalisar zartarwan jihar Kogi banda kaɗan kada ciki.

Bello ya ɗauki wannan matakin ne yayin da wa'adin mulkinsa na zango biyu ke dab da ƙarewa bayan zaɓen gwamna a watan Nuwamba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262